Sulhu da 'Yan Bindiga: Sheikh Gumi Ya Ragargaji Masu Sukarsa, Ya Fadi Nasarorin da Ya Samu

Sulhu da 'Yan Bindiga: Sheikh Gumi Ya Ragargaji Masu Sukarsa, Ya Fadi Nasarorin da Ya Samu

  • Wasu mutane sun dade suna kiraye-kirayen da a cafke Sheikh Ahmad Abubakar Gumi kan rawar da yake takawa wajen sulhu da 'yan bindiga
  • Sanannen malamin addinin Musuluncin ya fito ya ragargaji mutanen da ke kiran hukumomi su kama shi
  • Sheikh Gumi ya bayyana cewa abubuwan da yake yi, yana yin su ne domin ganin an samu zaman lafiya

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Kaduna - Shahararren malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, ya yi martani kan masu neman a kama shi saboda shiga sulhun da yake yi da 'yan bindiga.

Sheikh Gumi ya yi tur da irin kiran da wasu ke yi na a kama shi saboda tsokacin da yake yi kan batun ‘yan bindiga da tsaron kasa.

Sheikh Gumi ya kare kansa kan sulhu da 'yan bindiga
Sanannen malamin addinin musulunci, Sheikh Ahmed Abubakar Gumi Hoto: Dr. Ahmed Abubakar Mahmud Gumi
Source: Facebook

A cikin wani rubutu da ya wallafa a Facebook a ranar Lahadi, malamin ya fito ya kare kansa.

Kara karanta wannan

'Sai mun biya': Al'umma sun fadi makudan kudi da suke ba 'yan bindiga domin kariya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sheikh Gumi na shan suka

Sheikh Gumi, wanda tsawon shekaru yake taka rawa a matsayin mai shiga tsakanin gwamnati da ‘yan bindiga, ya sha samun yabo daga wasu da suka yi amince da hanyarsa, da kuma suka daga masu adawa da shi.

Wasu daga cikin masu suka suna tuhumarsa da kare ‘yan ta’adda, suna zargin cewa ya fi goyon bayan tattaunawa da su maimakon amfani da karfi.

Sheikh Gumi ya kira masu sukar nasa da mutane marasa mutunci, marasa tarbiyya, marasa kishin kasa, yana mai cewa sun fi son hayaniya da tada kura fiye da fuskantar gaskiya kan matsalar tsaro.

Sheikh Gumi ya soki masu sukarsa

Gumi ya yi Allah-wadai da kiraye-kirayen da ake yi na a kama shi, yana mai cewa bai aikata laifi ba, domin tattaunawa da ‘yan bindiga da nufin samar da zaman lafiya ba laifi ba ne.

Ya kara da cewa masu kira da a kama shi, son zuciya, jahilci da rashin jure ra’ayoyin wasu ne ke damunsu.

Kara karanta wannan

ADC ta yi mamakin matakin da Tinubu ya dauka bayan sabanin Wike da A.M Yerima

“A Kama shi!!! Waɗannan su ne kalmomin da marasa mutunci, marasa kishin kasa za su iya furtawa."

- Sheikh Ahmed Abubakar Gumi

Sheikh Gumi ya yi zargin cewa masu neman a kama shi sun mayar da kokarinsa na zaman lafiya batun siyasa maimakon nazarin tabarbarewar tsaron kasar.

Sheikh Gumi ya jagoranci sulhu da 'yan bindiga

Sheikh Gumi ya tunatar da yadda ya jagoranci wani babban shiri na tattaunawa a dajin Sabon Garin Yadi, karamar hukumar Giwa ta jihar Kaduna, a watan Janairun 2021.

Ya ce a wannan tafiyar, kwamishinan ’yan sanda na Kaduna a lokacin, wanda ya wakilci IGP, ya yi masa rakiya.

A cewarsa, taron ya samu halartar fiye da ‘yan bindiga 600 da shugabanninsu, domin shirin shigar da su cikin zaman lafiya da mika makamansu.

“Mun yi wa sama da ‘yan bindiga 600 wa’azi tare da shugabanninsu, kuma sun amince su ajiye makamai a kan gwamnati ta ba su tsaro da muhimman abubuwan more rayuwa."

- Sheikh Ahmed Abubakar Gumi

Sheikh Gumi ya kare kansa kan sulhu da 'yan bindiga
Sheikh Gumi a wajen sulhu da 'yan bindiga Hoto: Dr. Ahmad Abubakar Mahmud Gumi
Source: Facebook

Sheikh Gumi ya ce tattaunawar ta kasance karara, bisa doka, kuma da sanin hukumomi. Ya ce dukkan sharuddan da ‘yan bindigar suka gabatar, kamar samar da abubuwan more rayuwa da kariya daga kama su ba tare da dalili ba, ba a cika musu ba, wanda hakan ya sa tattaunawar ta rushe.

Kara karanta wannan

'Ka nemi kashe ni,' Wike ya yi martani mai zafi ga Buratai bayan rigima da soja

Gumi ya nuna takaici cewa maimakon mutane su tambayi dalilin da yasa gwamnati ta gaza aiwatar da yarjejeniyar, sai suka mayar da hankali wajen kai hari a kansa.

“Manufar wannan taro ita ce rage tashin hankali domin ‘yan bindiga su mika makamai su rungumi zaman lafiya."
"Fiye da 600 sun amince su ajiye makamansu, amma sharuddan da suka gabatar ba a aiwatar da su ba."

- Sheikh Ahmad Abubakar Gumi

Sheikh Gumi ya dage cewa duk abin da ya yi na cikin kishin kasa ne, don haka ya ga babu wani dalili da zai haifar da kiraye-kirayen kama shi.

Sheikh Gumi ya musanta tserewa zuwa Turkiyya

A wani labarin kuma, kun ji cewa Sheikh Ahmed Abubakar Mahmud Gumi, ya yi magana kan zargin ya tsere zuwa kasar Turkiyya.

Malamin addinin Musuluncin ya musanta cewa ya gudu zuwa Turkiyya saboda tsoron barazanar shugaban kasar Amurka, Donald Trump.

Sheikh Gumi ya bayyana cewa ko kadan ba tserewa ya yi ba, domin tun kafin Trump ya yi barazanarsa ya samu bizarsa zuwa Turkiyya.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng