Ana Batun Matashin Soja da Wike,Tinubu Ya Yi Magana kan Jarumtar Sojojin Najeriya

Ana Batun Matashin Soja da Wike,Tinubu Ya Yi Magana kan Jarumtar Sojojin Najeriya

  • Yayin da ake ci gaba da ce-ce-ku-ce kan abin da ya faru tsakanin sojan ruwa, A.M Yerima da Ministan Abuja, Tinubu ya yabawa dakarun sojoji
  • Shugaba Tinubu ya bayyana cewa dakarun sojojin Najeriya maza da mata sun cancanci yabo bisa sadaukarwar da suke yi wajen kare kasa
  • Bola Tinubu ya amince cewa Najeriya na fama da matsalar ta'addanci amma gwamnatinsa ta shirya tunkarar kowane kalubale

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya jinjinawa dakarun rundunar sojojin Najeriya mazansu da matansu bisa yadda suka bayar da rayuwarsu wajen kare kasa.

Wannan yabo na zuwa ne yayin da ake ta surutu kan matashin sojan ruwa, Laftanal A. M Yerima, wanda ya shafa kwalli a idonsa, ya hana ministan Abuja, Nyesom Wike shiga wani fili.

Kara karanta wannan

Laftanal Yerima: Abin da muka sani game da sojan ruwa da ya fatattaki Wike a Abuja

Sojoji da Bola Tinubu.
Hoton dakarun sojoji na daukar hoto da Shugaba Bola Ahmed Tinubu Hoto: @DHQNigeria
Source: Twitter

Tinubu ya jinjinawa sojojin Najeriya

Shugaba Tinubu ya ce sojoji sun cancanci yabo domin kara masu kwarin gwiwa duba da irin jajircewa da sadaukarwar da suke yi wajen tsare kasar nan, cewar rahoton Channels tv

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mai girma Bola Ahmed ya yabi sojojin ne yayin da yake jawabi a taron ƙungiyar editoci ta Nigerian Guild of Editors (NGE) a Abuja ranar Laraba, 12 ga Nuwamba, 2025.

Shugaba Bola Tinubu ya yi tambayoyi masu muhimmanci game da rawar da sojojin ke takawa wajen kare ƙasar nan dafa duk wani nau'i ma barazana.

Tambayoyin Tinubu ya yi kan aikin sojoji

Ya ce, la’akari da haɗarin da sojojin Najeriya ke fuskanta wajen kare iyakokin Najeriya, dole ne al’umma su nuna goyon baya da ƙarfafawa gare su, in ji Vanguard.

“Eh, muna fuskantar ƙalubale na ta’addanci, ‘yan fashi da sauran matsaloli, mun san haka. Shin muna yin wani abu game da hakan? Shin muna ƙarfafa sojojinmu? Shin muna karfafa musu gwiwa su ci gaba da yaƙi?

Kara karanta wannan

Wike ya gamu da gamonsa, soja ya ki bari ya tozarta shi a bainar jama'a

"Su na ba da rayuwarsu a fagen fama, wasu su jefa rayukansu cikin haɗari don kare ikon ƙasar nan. Wannan nauyi ne a wuyanmu duka,” in ji Tinubu.

Jawabin shugaban ƙasa Tinubu na zuwa ne yayin da ake ci gaba da nuna damuwa kan matsalolin tsaron da suka addabi sassan ƙasar nan, wanda ke jawo asarar rayuka.

Shugaban kasa, Bola Tinubu.
Hoton shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Source: Facebook

A ranar Alhamis da ta gabata, Shugaba Tinubu ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na zurfafa hulɗar ƙasa da ƙasa da ƙarfafa yaƙi da ta’addanci da aikata miyagun laifuka.

“Aikin da ke gaban mu babba ne. Amma mun ɗaura damarar tunkararsa cikin haɗin kai da ƙuduri, don mu kawar da ta’addanci kuma mu gina Najeriya mai wadata, haɗin kai da ƙarfi,” in ji shi.

Babachir ya soki Tinubu kan tsaro

A wani labarin, kun ji cewa Babachir Lawal ya zargi gwamnatin tarayya karkashin Shugaba Bola Tinubu da gazawa wajen magance matsalolin tsaro a kasar nan.

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya wanda ya yi aiki a gwamnatin marigayi Muhammadu Buhari, ya yi ikirarin cewa Tinubu ba shi da niyyar magance matsalar tsaro.

Kara karanta wannan

"Za a iya kifar da shi": Amaechi ya hango hanyar kifar da Tinubu a zaben 2027

Babachir Lawal ya kuma soki mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, yana cewa bai ga wani abin kirki da ya yi a ofishinsa ba.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262