Kwana Ya Kare: Babban Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Goni Imam Sa'id Ya Rasu

Kwana Ya Kare: Babban Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Goni Imam Sa'id Ya Rasu

  • Malamin addinin musulunci kuma limamin masallacim Izala na garin Funtua da ke jihar Katsina, Sheikh Goni Imam Sa'id ya kwanta dama
  • Sanatan Funtua (Katsina ta Kudu), Muntari Dandutse ya yi alhinin rasuwar shehin malamin a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin
  • Dantsute ya bayyana Sheikh Goni a matsayin mutumin kirki, wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen hidimta wa addinin musulunci

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Funtua, jihar Katsina - Babban malamin addinin musulunci a garin Funtua da ke jihar Katsina, Sheikh Goni Imam Sa'id Musa ya riga mu gidan gaskiya.

Marigayi malamin, wanda shi ne babban limamin masallacin 'yan izala da ke garin Funtua (JIBWIS) ya rasu ne ranar Lahadi da daddare bayan fama da jinya.

Sheikh Goni Imam Sa'id Musa.
Hoton marigayi limamin masallacim Izala a Funtua, Sheikh Goni Imam Sa'idu Musa Hoto: Senator Muntari Dandutse
Source: Facebook

Malamin Izala a Funtua ya rasu

Sanata mai wakiltar Katsina ta Kudu a Majalisar Dattawa, Muntaru Dandutse ya tabbatar da rasuwar malamin a wata sanarwa da ya wallafa a Facebook yau Litinin da safe.

Kara karanta wannan

"Abin da ya sa ƴan bindiga ke farmakar ƴan Najeriya," Gumi ya fito da wani zance

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rahotanni daga yankin sun nuna cewa za a yi jana'izarsa da misalin karfe 2:00 na rana yau Litinin a filin makarantar firamare ta Aya da ke cikin garin Funtua.

Sanata Muntari Dandutse bayyana jimaminsa kan rasuwar Sheikh Goni Imam Sa’idu Musa Funtua, tare da mika sakon ta'aziyya.

Musulmin Najeriya sun yi rashi

Ɗandutse ya ce rasuwar malamin babban rashi ne ga mutanen Funtua, Jihar Katsina, da kuma al'ummar musulmi baki daya.

Sanatan Funtua ya ce:

"Sheikh Goni Sa’idu Musa Funtua ya sadaukar da rayuwarsa wajen hidimar addinin Musulunci, yana koyar da Al-Qur’ani mai girma, fadakarwa da gina al'umma mai ilimi, zaman lafiya da kyawawan dabi’u.

Dandutse ya mika sakon ta'aziyya

Sanatan ya ƙara da roƙon Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta masa, Ya jikansa da rahama, Ya sa Aljanna ta zama makomarsa.

"Allah Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya jikansa da rahama. Ya ba iyalansa, ɗalibansa da al’umma haƙuri da juriya wajen jure wannan babban rashi," in ji shi.

Kara karanta wannan

Karin bayani: Ƴan bindiga sun farmaki dan majalisar Neja, an kashe jami'an tsaro

Sanata Muntari Dandutse.
Hoton Sanatan Katsina ta Kudu, Muntari Dantsue a zauren Majaliaar Dattawa Hoto: Sen. Muntari Dandutse
Source: Facebook

Ɗandutse ya ce rayuwar Sheikh Goni Liman Sa’idu Musa ta zama abin alfahari ga yankin Funtua da Jihar Katsina baki ɗaya saboda irin ayyukan alheri da ya bari a bayansa.

"Haka rayuwa take, kowa zai tafi, amma kyawawan ayyuka su ne gado na gaskiya. Sheikh Goni Liman Sa’idu Musa ya bar tarihi mai daraja,” in ji shi.

A ƙarshe, Sanata Ɗandutse ya roƙi Allah Ya jikansa, Ya sa kabarinsa ya zama lambun Aljanna, kuma Ya ba wa al’umma ikon bin sahunsa cikin kyawawan ayyuka.

Malamin musulunci a Kano ya rasu

A wani rahoton, kun ji cewa na'ibin babban limamin masallacin Jumma'a na Al-Furqan Kano, Malam Aminu Adam Dorayi ya riga mu gidan gaskiya.

Limamin masallacim Al-Furqan, Sheikh Bashir Aliyu Umar ya tabbatar da rasuwar Malam Aliyu Adam, tare da addu'ar Allah Ya jikansa.

utane da dama musamman jama'ar Kano sun tura sakon ta'aziyya da addu'ar Allah Ya jikan Malam Aminu Adam kuma ya gafarta masa kura-kuransa.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262