Malamin Addini Ya Gayawa Tinubu Gaskiya kan Mutanen da Ke Tare da Shi, Ya Ba Shi Shawara
- Shugaban cocin Redeemed Christian Church of God (RCCG), Fasto Enoch Adeboye, ya soki wasu daga cikin masu ba Mai girma Bola Tinubu shawara
- Fasto Enoch Adeboye ya nuna cewa wasu daga makusantan shugaban kasan ba sa sonsa saboda irin shawarwarin da suke ba shi
- Babban faston ya koka da cewa wasu daga cikinsu na Shugaba Tinubu gurguwar shawara wadda ba za ta amfane shi ba
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Shugaban cocin Redeemed Christian Church of God (RCCG), Fasto Enoch Adeboye, ya yi magana kan masu ba Shugaba Bola Tinubu shawara.
Fasto Enoch Adeboye ya bayyana damuwa kan cewa Shugaba Tinubu yana samun gurguwar shawara daga wajen wasu daga cikin masu ba shi shawara.

Source: Facebook
Jaridar Vanguard ta kawo rahoto cewa ya bayyana hakan ne yayin da yake wa’azi a taron addu’ar Holy Ghost na watan Nuwamba mai taken “The Eve of Glory".
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Babban faston ya nuna damuwarsa kan wani jawabi da Tinubu ya yi, inda ya tabo batun tsaron kasa.
Me Adeboye ya ce kan Tinubu
Fasto Adeboye wanda ya ambaci shugaban kasan a matsayin surikinsa, ya koka kan jawabin Tinubu inda ya ce tsaro ya inganta kuma mutanen da suka rasa gidajensu sun koma kauyukansu.
“Na kusan yin magana a watan da ya gabata lokacin da na ji jawabi daga surikina, shugaban kasa. Za ku iya komawa ku saurari jawabin, musamman ɓangaren da ya shafi tsaro."
"Lokacin da na ji ya ce komai ya daidaita yanzu, kuma mutanen da aka raba da gidajensu sun koma kauyukansu, na kusan cewa wanda ya rubuta wa shugabana, surikina, wannan jawabi, bai son sa.”
“Kuma idan za ku tambaye ni, ‘To ai shugaban kasa ne ya karanta jawabin,’ zan ce, shin bai duba abin da aka rubuta masa ba ne kafin ya karanta?"
"Idan haka ne, to akwai mutane da yawa a kusa da surikina da ba sa gaya masa gaskiya. A washegarin ranar, mun karanta a jarida cewa an kashe wani basarake, ko dai a Kwara ko a Kogi.”

Kara karanta wannan
Fasto Adeboye ya kawo mafita, ya aika sako ga Shugaba Tinubu kan barazanar Amurka
- Fasto Enoch Adeboye
Sai dai, Adeboye ya ce yanzu ba lokacin dora laifi bane, domin matsalar tsaro ta samo asali ne tun kafin gwamnatin Tinubu, rahoton jaridar The Punch ya tabbatar da labarin.
“Shugabanmu ya gaji wannan matsala, ta wanzu tun kafin shi. Amma ni a matsayina na masani a lissafi, abin da nake so shi ne mafita, ba dora laifi ba.”
- Fasto Enoch Adeboye

Source: Facebook
Adeboye ya ba Tinubu shawara
Faston ya ba da shawarar cewa gwamnati ta nemi hanyar diflomasiyya don roƙon Shugaban Amurka Donald Trump da ya ba Najeriya kwanaki 100 na rangwame don a samu damar tsara dabarun yaki da ta’addanci.
“A kira shugabannin tsaro duk da cewa sababbi ne, a ce su yi abin da ya dace cikin wata uku ko su yi murabus."
“Mun dade muna yi wa Najeriya addu’a, ba zai yiwu mu yi waɗannan addu’o’i da yawa ba tare da ganin wani canji ba.”
- Fasto Enoch Adeboye
Mukhtar Kabir ya goyi bayan kalaman da babban faston ya yi kan cewa mashawartan Tinubu ba sa gaya masa gaskiyar halin da ake ciki.
"Tabbas idan ka saurari sanarwowin da shugaban kasan yake fitarwa, za ka lura cewa kamar bai san abin da ke faruwa a kasa."
"Har yanzu akwai matsalar rashin tsaro, amma idan ka saurari bayanansa sai ka ji yana cewa al'amura sun gyaru."
"Tabbas ina ganin cewa mashawartan ba sa gaya masa gaskiya, kuma hakan abu ne mai hadari."
- Mukhtar Kabir
Tinubu ya gana da Sarkin Musulmi
A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya gana da Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar III.
Mai girma Tinubu ya gana da sarkin musulmin ne a fadar shugaban kasa da ke fadar Aso Rock a birnin Abuja.
Ganawar na cikin jerin tattaunawa da neman shawarwari da Shugaba Tinubu ke yi da shugabannin addini da na gargajiya a Najeriya kan barazanar da Amurka ta yi.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

