Babu Boye Boye, An Ji Dalilin da Ya Sa Bola Tinubu Bai Jawo Matarsa Ta Karbi Musulunci ba
- Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya halarci jana'izar mahaifiyar shugaban APC na kasa da aka yi yau Asabar a jihar Filato
- A jawabinsa a cikin coci a Jos, Tinubu ya bayyana dalilin da ya sa bai nemi musuluntar da matarsa, Sanata Oluremi Tinubu ba
- Ya ce tasowa ya yi ya samu iyayensa suna bin tafarkin addinin musulunci kuma bai canza ba, amma matarsa fasto ce
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Plateau - Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana dalilinsa na kyale matarsa ta yi addinin kiritanci, da kuma yadda suke zaune lafiya cikin mutunta juna.
Shugaban Bola Tinubu ya ce bai taba jaraba jawo hankalin Oluremi Tinubu, uwargidan shugaban kasa, domin ta shiga addinin Musulunci ba.

Source: Twitter
Tribune Nigeria ta tattaro cewa Tinubu ya ce ya yi imani da soyayya, 'yancin addini da mutunta juna tsakanin mabiya addinai daban-daban.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Tinubu ya yi wannan bayani ne a ranar Asabar a wurin jana’izar Nana Lydia Yilwatda, mahaifiyar shugaban jam’iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda da aka gudanar a coci a Jos, jihar Filato.
Tinubu da matarsa ba addininsu guda ba
Shugaban kasar, wanda ya isa Jos da misalin karfe 2 na rana domin halartar jana'izar, ya ce a cikin musulunci aka haife shi shiyasa ya zama musulmi.
Ya kara da cewa shi da uwargidansa suna bauta wa Allah guda daya, kuma a karshe za su amsa tambayoyi a gabanSa.
Abin da ya fi muhimmanci, a cewarsa, shi ne ayyukan mutane, halinsu da kaunar da suke nuna wa juna.
Tinubu ya bukaci ‘yan Najeriya da su rungumi hakuri da zaman lafiya a tsakaninsu, yana mai jaddada kiyayya ba ta da wani amfani.
Mai Girma Shugaban Kasa Ya kuma yi addu’a Allah ya ji kan Lydia Yilwatda tare da ba iyalinta hakuri da albarka.
Abin da ya hana Tinubu musuluntar da matarsa
Da yake bayanin abin da ya sa bai yi kokarin musuluntar da matarsa ba, Shugaba Tinubu ya ce.
"Duk abin da Allah ya kaddaro babu mahalukin da zai iya canza shi, ni musulmi ne, tasowa na yi naga musulunci a wurin iyaye na, kuma ban canza ba.
"Amma matata fasto ce, muna mutunta juna, tana mani addu'a, ba mu taba sabani kan addini ba. Ban taba kokarin musuluntar da ita ba saboda na yarda da 'yancin addini.
"Allah Madaukakin Sarki daya ne, duk shi muke bauta wa muna rokonsa, wata rana Shi zai mana hisabi kan ayyukan da muka aikata."

Source: Twitter
Tinubu ya yi magana kan soke faretin soji
A wani labarin, kun ji cewa Shugaba Bola Tinubu ya ce soke faretin cikar Najeriya shekara 65 da 'yanci ya ba shi damar yin barci mai dadi a daren 1 ga Oktoba, 2025.
Tun farko, gwamnatin tarayya ta sanar da soke bikin faretin sojoji da aka shirya gudanarwa a ranar Laraba domin tunawa da ranar ’yancin kai.

Kara karanta wannan
Gwamnatin Tinubu ta yi martani kan zargin jefa 'yan Najeriya miliyan 15 a bakin cikin talauci
Shugaba Tinubu ya ce soki faretin ya ba shi damar samun nishadi da barci mai dadi duk da dai hakan ya karya tarihin faretin ranar samun yancin kai.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Asali: Legit.ng

