Bayan Soke Fareti, Tinubu Ya Fadi abin da Ya Faru da Shi a Daren 1 ga Oktoba 2025

Bayan Soke Fareti, Tinubu Ya Fadi abin da Ya Faru da Shi a Daren 1 ga Oktoba 2025

  • Shugaba Bola Tinubu ya ce soke faretin cikar Najeriya shekara 65 da 'yanci ya ba shi damar yin barci mai dadi a daren 1 ga Oktoba, 2025
  • Shugaban kasar, ya kuma ce ya samu damar jin daɗin karin kumallo a ranar Laraba, har ya shirya zuwa kaddamar da cibiyar Wole Soyinka
  • Tinubu ya bayyana Wole Soyinka a matsayin babbar kadara ga Najeriya, yana mai cewa ya ba da gudummawa wajen kwato 'yancin kasa

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Legas - Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi bayani game da soke faretin da aka saba yi na bikin murnar cikar Najeriya shekara 65 da samun ’yancin kai.

A cewar shugaban kasar, soke faretin ranar 1 ga Oktoba ya ba shi damar yin barci mai dadi tare da jin daɗin karin kumallo a safiyar Laraba.

Kara karanta wannan

Tazarce: An zakulo manyan abubuwa 6 da za su taimaka wa Tinubu ya ci zabe a 2027

Shugaba Bola Tinubu ya ce ya yi barci mai dadi a daren ranar 1 ga Oktoba, 2025
Shugaba Bola Tinubu tare da uwargidansa a bikin kaddamar da cibiyar Wole Soyinka, a Legas. Hoto: @officialABAT
Source: Twitter

Gwamnati ta soke faretin ranar 'yanci

A cewar jaridar Daily Trust, gwamnatin tarayya ta sanar da soke bikin faretin sojoji da aka shirya gudanarwa a ranar Laraba, 1 ga Oktoba, 2025 domin tunawa da ranar ’yancin kai.

Sanarwar sokewar bikin ta fito ne daga ofishin sakataren gwamnatin tarayya (SGF) a ranar Litinin, kamar yadda Legit Hausa ta rahoto.

Sakataren gwamnatin ya jaddada cewa ba a soke faretin da nufin rage muhimmancin bikin shekara 65 da samun ’yancin kan Najeriya ba.

Sanarwar ta ce:

"Gwamnatin Tarayya na sanar da soke bikin tunawa da ranar ’yancin kai ta bana da aka tsara gudanarwa ranar Laraba, 1 ga Oktoba. Wannan mataki ba ya nufin rage darajar wannan muhimmiyar rana a tarihin kasa."

Tinubu ya gode wa CBN da kwamitin BC

Tinubu ya yi jawabi game da soke fareti ne yayin da yake jawabi a wurin taron kaddamar da sabuwar cibiyar al'adu da kere-kere ta Wole Soyinka a Legas.

Kara karanta wannan

'Za ki warke': An kama malamin addini kan zargin kwanciya da budurwa na kwana 7

A wajen kaddamar da cibiyar, wacce aka fi sani a baya da cibiyar NAT, Shugaba Tinubu ya bayyana cewa ya samu hutu sosai bayan soke bikin faretin.

Ya kuma bayyana cewa an samu karin nishaɗi a bikin kaddamar da cibiyar, wacce CBN tare da kwamitin ma'aikatan bankuna suka dauki nauyin gyara da sabuntawa.

“Na samu barci mai dadi” – Tinubu

Tinubu ya bayyana farin cikinsa kan yadda aka sake bude ginin, wanda ya ce ya cancaci sunan Wole Soyinka, gwarzon marubuci kuma mai lambar yabo ta duniya.

Shugaban kasa Bola Tinubu ya ce:

"Na gode kwarai da wannan daren. Na yi barci cikin salama, na yi karin kumallo mai dadi sannan na jira lokacin wannan bikin. Na aiwatar da abubuwa masu muhimmanci a daren nan."

Ya kara da cewa wannan ya karya tarihin jerin gwanon shagulgulan faretin sojoji da aka saba yi a duk ranar zagayowar ’yancin kai.

Shugaba Bola Tinubu ya yabawa Farfesa Wole Soyinka a ranar 'yancin kai
Shugaba Bola Tinubu yana rattaba hannu kan wata takarda a filin Eagle Square, Abuja. Hoto: @officialABAT
Source: Twitter

Wole Soyinka a matsayin gwarzon kasa

Da yake yabon marubucin, Tinubu ya ce Wale Soyinka babbar kadara ce ga duniya, musamman Najeriya, wanda ya bayar da gudummawa wajen gina kasa da kuma fafutukar ’yanci.

Kara karanta wannan

Gwamna Fintiri ya yi afuwa ga masu laifi don murnar cikar Najeriya shekara 65 da samun 'yanci

A sanarwar da ya fitar a shafinsa na X, Tinubu ya ce:

"Na tabbatar babu wani suna da ya dace da wannan gini face 'Cibiyar Wole Soyinka,' kuma ya zama dole a yi hakan."

Manyan bakin da suka halarci bikin sun hada da uwargidan shugaban kasa, Oluremi Tinubu, Gwamna Babajide Sanwo-Olu, Godswill Akpabio, da kuma sarkin Kano Muhammadu Sanusi II tare da Farfesa Wole Soyinka wanda aka karrama.

'An fara samun sauki a Najeriya' - Tinubu

A wani labarin, mun ruwaito cewa, Shugaba Bola Tinubu ya ce lokacin matsananciyar wahala ta kau a Najeriya, za a fara ganin ribar manufofinsa.

Ya bayyana haka ne a lokacin da ya ke jawabi ga 'yan kasa kan cikar kasar nan shekaru 65 da samun 'yancin kai daga Turawa.

A cewarsa, Najeriya ta fara fitowa daga cikin mawuyacin halin tattalin arziki da ta tsinci kanta ciki a baya, tare da yi wa jama'a albishir.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com