Kurunkus: Kotu Ta Yanke Hukunci kan Ingancin Dokar Ta Bacin da Tinubu Ya Sa a Ribas

Kurunkus: Kotu Ta Yanke Hukunci kan Ingancin Dokar Ta Bacin da Tinubu Ya Sa a Ribas

  • Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi nasara a karar da aka kalubalanci dokar ta-bacin da ya ayyana a jihar Ribas tun watan Maris, 2025
  • Babbar Kotun Tarayya mai zama a Abuja ta yi fatali da kasar, tana mai cewa masu kara sun gaza habatar da hujja fiye da ta gwamnatin tarayya
  • Alkalin Kotun na Tarayya ya ce masu karar ba su da hurumin kalubalantar matakin, kuma kotun koli ce ke kadai ke da ikon sauraron batun

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Babbar Kotun Tarayya Mai Zama a Abuja ta yi fatali da karar da aka shigar ta kalubalantar dokar ta-bacin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sa a jihar Ribas.

Mai shari’a James Omotosho ne ya yanke wannan hukunci, inda ya yi watsi da karar da aka shigar kan ayyana dokar ta-baci da Tinubu ya yi a Jihar Ribas a ranar 18 ga Maris, 2025.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu ta yi martani kan zargin jefa 'yan Najeriya miliyan 15 a bakin cikin talauci

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu.
Hoton Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban kasa da ke Abuja. Hoto: @DOludegun
Source: Twitter

Matakan da Bola Tinubu ya dauka a Ribas

Leadership ta tattaro cewa bayan ayyana dokar ta baci, Tinubu ya kuma dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara da ’yan majalisar dokokin jihar na tsawon watanni shida.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sannan kuma shugaban kasa ya nada shugaban riko domin kula da harkokin jihar Ribas na tsawon wannan lokacin.

Sakamakon rashin gamsuwa da wannan mataki, Belema Briggs da wasu mutum huɗu suka kalubalanci Tinubu a kotu, inda suka yi zargin cewa wannan mataki ya tauye musu ’yancinsu.

Hukuncin da Kotun Abuja ta yanke

A hukuncin da ya yanke yau Alhamis, Mai shari’a Omotosho ya bayyana cewa masu shigar da karar ba su da hurumin doka da zai ba su damar shigar da kara a gaban kotu.

Bugu da kari, alkalin ya bayyana cewa kotun koli ce kaɗai ke da ikon yanke hukunci kan irin wannan batu.

Mai shari’ar ya kara da cewa masu karar sun gaza kawo shaidar cewa suna daga cikin yan Majalisar Dokokin Ribas ko mambobin Majalisar Zartarwa ta jiha (SEC).

Kara karanta wannan

"Mun ceto Naira," Tinubu ya tabo batun darajar kudin Najeriya a jawabin ranar 'yanci

A cewar alkalin, hakan ya sa masu karar suka gaza gamsar da kotu cewa matakin ayyana dokar ta-bacin ya cutar da su fiye da yadda ya cutar da jama'ar Ribas.

Abubuwan da kotu ta gano a shari'ar

Hukuncin da kotun ta yanke ya nuna cewa masu karar sun shigar da korafi gaban kotu ba tare da amincewar Antoni Janar na jihar Ribas kuma kwamishinan shari'a ba.

Mai shari’a Omotosho ya ce babu wanda ya iya kawo hujjar da ta take hujjar Shugaba Tinubu cewa ya ayyana dokar ta-bacin ne domin dakile tashin rikici da barazana ga tsaro.

Shugaba Tinubu da Gwamna Fubara.
Hoton Shugaba Tinubu da Gwamna Fubara na Ribas. Hoto: @OfficialABAT, Sir Siminalayi Fubara
Source: Twitter

Ya kammala da cewa karar “ba ta da tushe kuma ba ta da amfani” domin masu shigar da ita ba su da goyon bayan jama’ar Jihar Ribas, wannan ya sa ya kori karar gabata daya.

Shugaba Tinubu ya gana da gwamnan Ribas

A wani labarin, kum ji cewa Gwamna Simi Fubara na jihar Ribas ya lai ziyara fadar shugaban kasa awani kadan bayan Tinubu ya maida shi kan mulki.

Gwamnan ya samu ganawa da Shugaba Bola Tinubu ya sirrance, inda ake kyautata zaton sun tattauna ne kan batutuwan da suka shafi Ribas.

Kara karanta wannan

Nigeria @65: Muhimman abubuwa 5 da Tinubu ya fada a jawabin ranar samun 'yanci

Fadar Shugaban Kasa da Gwamna Fubara ba su bayyana ainihin abin da shugabannin biyu suka tattauna a hukumance ba.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262