An Shiga Jimami bayan Ramin Hakar Ma'adanai Ya Rufta da Mutane Sama da 100 a Zamfara

An Shiga Jimami bayan Ramin Hakar Ma'adanai Ya Rufta da Mutane Sama da 100 a Zamfara

  • Mummunan ibtila'i ya ritsa da wasu mutanen da suka fita zuwa wajen aikin hakar ma'adanai a jihar Zamfara
  • Lamarin ya auku ne bayan da wani ramin haka ma'adanai ya rufta kan ma'aikata a karamar hukumar Maru, wanda hakan ya jawo asarar rayuka
  • Majiyoyi sun bayyana cewa akwai sama da mutane 100 a cikin ramin hakar ma'adanan lokacin da ya rufta musu

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Zamfara - Ana fargabar fiye da mutum 100 sun mutu sakamakon ruftawar wani ramin hakar zinare a jihar Zamfara.

Mutanen da suka tsira daga lamarin da kuma mazauna yankin su ka bayyana hakan.

Ramin hakar ma'adanai ya rufta a Zamfara
Taswirar jihar Zamfara, tarayyar Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Jaridar The Nation ta ce lamarin ya auku ne a wani rami da ke wajen hakar ma’adanai na Kadauri, a karamar hukumar Maru.

Rami ya ruguje da mutane a Zamfara

Ramin ya ruguje ne a ranar Alhamis yayin da daruruwan ma’aikatan hakar ma’adanai ke aiki a karkashin kasa.

Kara karanta wannan

Kazamin rikicin manoma ya firgita Darazo, ya hana zuwa gona a Bauchi

Rahotanni sun bayyana cewa ana ci gaba da aikin ceto har zuwa daren jiya Juma'a.

Sanusi Auwal, Wani mazaunin yankin da ya shiga cikin aikin ceto, Sanusi Auwal, ya bayyana cewa an riga an fitar da gawarwaki akalla 13 daga cikin ramin da ya ruguje, ciki har da na ɗan uwansa.

"Fiye da ma’aikatan hakar zinare 100 ne ke cikin ramin lokacin da ya ruguje."

- Sanusi Auwal

Wani wanda ya tsira, Isa Sani, wanda ke samun kulawar likitoci saboda raunukan da ya samu, ya bayyana cewa Allah ne ya kubutar da su.

"Mun yi sa’a da aka ceto mu da ranmu. Daga cikin fiye da mutum 100, mu 15 ne kawai aka ciro da ransu."

- Isa Sani

Wasu mutane sun tsira daga ramin

Wani ganau, Sani Hassan, wanda ya sha da kyar, ya shaidawa jaridar Punch cewa yana daga cikin wadanda suka samu sa'ar tsira da ransu.

A cewarsa, yana aikin hakar zinare ne a cikin ramin a ranar Alhamis lokacin da ya fito don shan ruwa.

Kara karanta wannan

Asiri ya tonu: Gwamnatin katsina ta gano ma'aikatan bogi sama da 3,000

"Jim kaɗan bayan na fito daga ramin hakar zinaren, sai kawai ya ruguje yayin da abokan aikina da dama ke ciki."

- Sani Hassan

Mai magana da yawun ‘yan sandan Zamfara, Yazid Abubakar, bai amsa kira da sakonnin da aka tura masa domin jin ta bakinsa ba.

Ramin hakar ma'adanai ya rufto kan mutane a Zamfara
Hoton gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Karanta wasu labaran kan hakar ma'adanai

'Yan bindiga sun kai hari a Zamfara

A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu miyagun 'yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a jihar Zamfara.

'Yan bindigan sun kai harin ne a wani kauye mai suna Bayan Dutsi da ke yankin Tofa a karamar hukumar Bungudu ta jihar.

Tsagerun 'yan bindigan sun jikkata mutane uku tare da yin awon gaba da wasu mutane da dama wadanda ba a san adadinsu ba a yayin harin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng