‘Sau 2 ba Mu Sallar Juma’a’: Musulmai Sun Roki Sauya Ranar Nadin Sarki da Za a Yi

‘Sau 2 ba Mu Sallar Juma’a’: Musulmai Sun Roki Sauya Ranar Nadin Sarki da Za a Yi

  • Kungiyar MURIC ta yi Allah wadai kan sanya ranar nadin Sarki da za a yi a karshen watan Satumbar wannan shekara ta 2025
  • MURIC ta bukaci dage bikin mika sandar sarautar Sarkin Ibadan da aka shirya ranar Juma’a, saboda zai hana Musulmi gudanar da Sallah
  • Farfesa Ishaq Akintola ya tuna matsalolin da Musulmi suka sha samu a baya kan wannan matsala da ta taba tasowa a baya

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Ibadan, Oyo - Kungiyar Kare Hakkokin Musulmi ta Kasa (MURIC) ta yi kira da a dage bikin miƙa sandar sarauta da aka shirya a ranar Juma'a.

Kungiyar ta bayyana damuwa kan yawan matsaloli da Musulmi suka samu a baya game da irin wannan biki da aka yi.

MURIC ta yi gargadi kan nada Sarkin Ibadan
Sabon Sarkin Ibadan mai jiran gado, Rashidi Ladoja da shugaban MURIC, Ishaq Akintola. Hoto: Seyi Makinde, Ishaq Akintola.
Source: Facebook

Rahoton Aminiya ya ce shugaban kungiyar, Farfesa Ishaq Akintola shi ya bukaci daga ranar bikin domin mutunta mabiya addinin Musulunci.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu zai yi jawabi kai tsaye ga 'yan Najeriya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yaushe za a gudanar bikin nadin Sarkin Ibadan?

Hakan ya biyo bayan shirin nada sabon Sarkin Ibadan da aka fi sani da Olubadan da aka shirya ranar Juma’a wanda ya jawo suka musamman saboda muhimmancin ranar.

Hukumomi sun shirya gudanar da bikin ne a ranar 26 ga watan Satumar 2025 da muke ciki bayan mutuwar marigayi tsohon Sarki.

Rahotanni daga jihar Oyo sun nuna cewa Gwamna Seyi Makinde ya amince da nadin sabon Sarkin a matsayin Olubadan na 44.

Tsohon gwamna zai dare kujerar sarauta

Wannan dai na zuwa ne bayan rasuwar tsohon Sarkin Ibadan, Oba Owolabi Olakulehin, a jihar da ke Kudu maso Yammacin Najeriya.

Majalisar masu nada Sarki na Olubadan ta zabi tsohon gwamna Rashidi Ladoja a matsayin wanda zai maye gurbin marigayi.

Masu nadin sarautar sun dauki matakin saka sunan Ladoja ne a Ibadan duk da cewa bai halarci taron da aka gudanar ba.

Kara karanta wannan

Tinubu da kansa ya fadi abubuwan da ya tattauna da shugaban Kasar Faransa

MURIC ta caccaki shirin nada sabon Sarki ranar Juma'a
Shugaban kungiyar kare hakkin Musulmi, MURIC, Farfesa Ishaq Akintola. Hoto: Ishaq Akintola.
Source: Twitter

Nadin sarauta: MURIC ta dauki zafi a Oyo

Sai dai kungiyar MURIC ta yi Allah wadai da sanya ranar Juma'a wanda ya yi daidai da lokacin da Musulmai ke gudanar da addu'o'insu.

Shugaban ƙungiyar, Farfesa Ishaq Akintola, ya ce:

"Sau biyu irin wannan matsala ta faru a baya, inda Musulmi suka kasa gudanar da Sallar Juma’a."

Wane zargi MURIC ke yiwa Gwamna Makinde?

MURIC ta kuma soki Gwamna Seyi Makinde da kokarin mayar da ranar Juma'a a matsayin ranar da ya ware domin yin wasu bukukuwa.

Akintola ya kara da cewa:

"MURIC ba za ta amince da yunƙurin mayar da Juma’a ranar bukukuwan Kiristoci ba."

Saboda haka ya bukaci a mayar da Juma’a ranar addu’o’in Musulmi domin girmama sabon Sarkin Ibadan, ko kuma a dage bikin zuwa Asabar.

MURIC ta zargi jami'a da tilasta Musulmai zuwa coci

Kun ji cewa Kungiyar MURIC ta zargi jami’ar Adeleke da hana dalibai Musulmi gudanar da ibadun Ramadan, ana tilasta musu halartar coci.

Kara karanta wannan

Da gaske an kwace sarautar da Sarki ya ba Shugaba Tinubu a Arewa? Gaskiya ta fito

MURIC ta ce jami’ar ta katse sallar tarawihi da dalibai suka gudanar, tare da gargaɗinsu da kada su sake yin hakan a harabar makarantar.

Kungiyar ta bukaci NUC da ta binciki dokokin jami’ar, tana mai cewa an haramta sallah da sanya hijabi, kuma ana tauye ‘yanci.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.