Akwai Kura: Malami Ya Yi Hasashe Shugabannin Kasashen da Za a Iya Sacewa a Afrika

Akwai Kura: Malami Ya Yi Hasashe Shugabannin Kasashen da Za a Iya Sacewa a Afrika

  • Fasto Babatunde Elijah Ayodele ya yi gargadi ga shugabanni a Afrika bayan ya yi hasashen wani abu da zai iya faruwa da su
  • Ya shawarci shugabannin kasashen Côte d’Ivoire da Kamaru kan su kara tsaurara matakan tsaro
  • Malamin addinin ya kuma ce shugaban kasan Faransa, Emmanuel Macron, na da wani shirin boye kan kasashen Afrika da dama

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Legas - Shugaban cocin INRI Evangelical Spiritual Church, Primate Babatunde Elijah Ayodele, ya yi gargadi ga shugabannin Afrika.

Primate Ayodele ya bayyana cewa wasu 'dakaru na musamman' na iya yin garkuwa da shugaban wata kasa a nahiyar Afrika.

Primate Ayodele ya yi hasashe kan shugabannin Afrika
Hoton Primate Babatunde Elijah Ayodele, yana jawabi a coci Hoto: Primate Babatunde Elijah Ayodele
Source: Facebook

Jaridar Tribune ta kawo rahoto cewa hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai taimakawa malamin addinin kan harkokin yada labarai, Osho Oluwatosin, ya fitar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wane hasashe aka yi kan shugabannin Afrika?

Kara karanta wannan

Da gaske an kwace sarautar da Sarki ya ba Shugaba Tinubu a Arewa? Gaskiya ta fito

Primate Ayodele ya ce ya hango shugabannin kasashe wadanda suka kwashe lokaci a kan mulki, suna cikin hadarin fuskantar hakan.

Ya yi kira musamman ga shugabannin kasashen Côte d’Ivoire da Kamaru, wadanda suka shafe shekaru sama da 10 a kan karagar mulki, da su yi taka-tsantsan.

"Na hango shugaban wata kasa a Afrika zai iya fadawa tarkon yin garkuwa da shi. Ban san yadda zai faru ba, amma na ga wasu sojoji na musamman suna yi wa shugabannin kasashen da suka daɗe a mulki barazana."
"Dole ne shugabannin kasashen Cote d'Ivoire da Kamaru su yi taka tsan-tsan kan hakan"

- Primate Babatunde Elijah Ayodele

Malami ya hango makircin Emmanuel Macron

Hakazalika, Primate Ayodele ya yi ikirarin cewa shugaban kasan Faransa, Emmanuel Macron na da wani shiri da zai illata kasashen Afrika da dama.

Ya ce daga cikin kasashen har da Jamhuriyar Benin, Burkina Faso, Mali, Nijar, Burundi da Senegal, rahoton jaridar Independent ya tabbatar da labarin.

Malamin addinin ya gargadi shugabannin wadannan kasashe, da su zage damtse wajen kare kansu da kasashensu daga shirin kasashen Yammacin duniya na sake maida Afrika tamkar mallakarsu.

Kara karanta wannan

'Abubuwa 4 ne ke rura wutar ta'addanci,' Gwamna Uba Sani ya nemo mafita ga Arewa

Primate Ayodele ya gargadi shugabannin wasu kasashe a Afrika
Hoton Primate Babatunde Elijah Ayodele, yayin wa'azi a coci Hoto: Primate Babatunde Elijah Ayodele
Source: Twitter
"Macron na da wani shiri da zai lalata kasashe da dama a Afrika, dole shugabannin Benin, Burkina Faso, Mali, Nijar, Burundi da Senegal su kula."
"Ana son a sake bautar da Afrika, dole ne shugabannin kasashe su zage damtse don kare nahiyar daga fadawa hannun Turawan Yamma."

- Primate Babatunde Elijah Ayodele

Wannan sabon hasashen na Primage Ayodele na zuwa ne bayan wani gargadi da ya taba yi cewa nan da shekaru 20 masu zuwa matasa za su tayar da wata gagarumar guguwa ta juyin-juya hali a fadin nahiyar Afrika.

Ayodele ya yi hasashe kan tazarcen Tinubu

A wani labarin kuma, kun ji cewa babban malamin addinin Kirista, Babatunde Elijah Ayodele, ya yi hasashe kan tazarcen shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, a zaben 2027.

Primate Ayodele ya ja kunnen Shugaba Tinubu kan cewa akwai wasu mutane uku da za su iya kifar da shi.

Kara karanta wannan

"Yaudara ce": Gwamna Uba Sani ya fallasa 'yan siyasa kan matsalar rashin tsaro

Malamin addinin ya bayyana cewa daga cikin wahayin da aka yi masa na mutanen da za su iya kayar da Tinubu, babu tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathana cikinsu.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng