Rikici Ya Barke a Wurin Taron Sarakuna da Aka Nemi Gwamna Ya Tsige Sarki a Najeriya
- Rikici ya barke a yunkurin tsige Sarkin Ipetumodu, wanda kotun kasar Amurka ta daure tsawon watanni 56 a gidan yari
- A wani taro da aka shirya a masarautar Sarkin da ke jihar Osun, masu nadin Sarki da 'yan gidan sarauta sun tashi baram-baram
- Wannan lamari dai na zuwa ne bayan kira ga Gwamnan Osun ya sauke Sarkin saboda hukuncin da kotun Amurka ta yanke masa
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Osun - Rikici ya barke tsakanin 'ya'yan gidan sarauta na masarautar Ipetumodu a wurin wani taron da suka gudanar a jihar Osun.
Hakan dai na zuwa ne bayan kiran da aka yi ga Gwamna Ademola Adeleke da ya tsige Sarkin Ipetumodu, Oba Joseph Oloyede saboda hukuncin da aka yanke masa a Amurka.

Source: Twitter
Punch ta tattaro a makonnin da suka shige ne aka yanke wa Oba Oloyede, wanda shi ne Apetumodu na 27 a masarautar Ipetumodu hukuncin daurin shekaru sama da hudu a gidan yari a Amurka.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Kotun Amurka ta yanke masa wannan hukunci ne kan kama shi da laifin cinye kudin tallafin COVID-19 da ya karba ta hanyar amfani da bayanan karya.
Rikici ya barke a taron sarakuna a Osun
Wannan ya sa masu zaben Sarki da sauran 'yayan gidan sarautar suka fara tarurruka da nufin tattaunawa kan makomar Sarkin don daukar matakin da ya dace
An ruwaito cewa sarakunan yankin sun kira wani taro, wanda aka gudanar a fadar masarautar karkashin jagorancin Asalu na Ipetumodu, Cif Sunday Adedeji.
Bayanai sun nuna cewa an fara taron da misalin ƙarfe 4:00 na yammacin jiya Talata ba tare da wata matsala ba, har sai da wani ɗan gidan sarauta ya nemi a rubuta wasika a hukumance zuwa ga Gwamna Adeleke.
An fara neman gwamnan Osun ya tsige Sarki
Ya bukaci Adedeji, wanda shi ne shugaban masu nadin sarki, da ya rubuta takarda zuwa ga Gwamna Adeleke domin neman ya ayyana kujerar sarkin da babu kowa a kanta.
Sai dai Adedeji ya ki amincewa da wannan bukata, inda ya sanar da cewa ba zai shiga cikin irin wannan yunkuri ba.
Wannan ne ya tayar da ce-ce-ku-ce da hayaniya tsakanin mahalarta taron, abin da ya sa taron ya tarwatse da misalin ƙarfe 6:00 na yamma, in ji rahoton PM News.

Source: Facebook
Wace matsala aka cimma a taron masarauta?
Bayan taron, wani ɗan sarauta daga gidan Aribile, Olaboye Ayoola, ya nuna rashin jin daɗinsa da yadda Adedeji ya ƙi amincewa da matsayar da aka cimma a taron.
“Mun cimma matsaya cewa a zabi sababbin masu nada Sarki guda biyu domin maye gurbin waɗanda suka rasu sannan a rubuta takarda zuwa ga gwamna, a nemi ya tsige Sarki," in ji shi.
Amma Cif Adedeji ya ƙi amincewa, sannan ya sanar da cewa ba shi da sha’awar ci gaba da zama mai nada sarauta, "wannan ya jawo rikici, taron ya tarwatse ba tare da cimma matsaya ba.”
Da aka tuntube shi, Adedeji ya tabbatar da ƙin amincewarsa da wannan bukata, inda kawai ya ce: “Eh, gaskiya ne. Amma dole zaman lafiya ya tabbata da farko.”

Kara karanta wannan
"Mun gano tushen matsalar": Gwamna Uba Sani ya fadi dalilin sulhu da 'yan bindiga
Gwamna Adeleke na tunanin tsige Sarki
A wani rahoton, kun ji cewa Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun na duba yiwuwar tsige Mai Martaba Sarkin Ipetumodu, Oba Joseph Oloyede.
Hakan dai na zuwa ne bayan kotun Amurka ta yanke wa sarkin hukuncin zaman gidan yari na tsawon watanni 56.
Rahotanni sun nuna cewa matukar ba a samu wani sauyi daga baya ba,.Gwamna Adeleke zai tube wa Sarkin rawani sakamakon laifin da ya aikata a Amurka.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

