"Mun Gano Tushen Matsalar": Gwamna Uba Sani Ya Fadi Dalilin Sulhu da 'Yan Bindiga

"Mun Gano Tushen Matsalar": Gwamna Uba Sani Ya Fadi Dalilin Sulhu da 'Yan Bindiga

  • Gwamnan jihar Kaduna, ya fito ya yi magana kan matakin da gwamnatinsa ta dauka na yin sulhu da 'yan bindiga
  • Uba Sani ya bayyana cewa sai da su ka gudanar da bincike don gano ainihin abubuwan da suke haddasa matsalar rashin tsaro
  • Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa dole ne shugabanni su dauki alhaki kan matsalar rashin maimakon dora laifin a kan wasu

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Kaduna - Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya yi magana kan shirin sulhu don samun zaman lafiya da gwamnatinsa ta bullo da shi.

Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa shirin ya haɗa sarakunan gargajiya, shugabannin addini da sauran masu ruwa da tsaki.

Gwamna Uba Sani ya yi magana kan rashin tsaro
Hoton Gwamna Uba Sani na jawabi a wajen taron kungiyar Izala Hoto: Senator Uba Sani
Source: Facebook

Gwamna Uba Sani ya bayyana hakan yayin da jawabi a wajen wani taro da kungiyar Izala ta shirya a Kaduna, cewar rahoton jaridar Vanguard.

Kara karanta wannan

"Yaudara ce": Gwamna Uba Sani ya fallasa 'yan siyasa kan matsalar rashin tsaro

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wadanne matsaloli suka haddasa rashin tsaro?

Uba Sani kawo misali da Birnin Gwari, inda Sarkin ya jagoranci kokarin da ya haifar da zaman lafiya bayan shafe watanni shida ana tattaunawa domin fahimtar ainihin dalilan rashin tsaro.

"Mun gano cewa talauci, rashin ayyukan yi, karancin makarantu, asibitoci, da harkokin kasuwanci a karkara ne suka tura mutane cikin aikata laifi."

- Gwamna Uba Sani

Gwamna Uba Sani ya jaddada cewa dole ne shugabanni su ɗauki alhakin matsalar tsaro maimakon jefa laifi kan wasu, rahoton jaridar Daily Trust ya tabbatar.

Megasa Uba Sani ya yi sulhu da 'yan bindiga?

"Bai kamata mu yaudari jama’armu ta hanyar cewa Shugaba Tinubu ko mai ba da shawara kan harkokin tsaro na kasa, Nuhu Ribadu, su ne masu alhakin matsalar ba."
"Bai kamata mu sa ran za su je Giwa, Birnin Gwari ko dajin Dansadau don su magance mana matsalar ba. Mu ne jama’a suka zaɓa, kuma mu ne ke da alhakin yin duk mai yiwuwa don kare mutanenmu.”

Kara karanta wannan

Bayan shan suka, Gwamna Buni ya magantu kan Malam Nata'ala, ya ɗauki alkawari

"Na yanke shawarar ɗaukar hanyar yin sulhu a Kaduna wajen magance matsalar tsaro, saboda ni Allah zai tambaya a ranar lahira."

- Gwamna Uba Sani

Uba Sani ya fadi dalilin yin sulhu
Hoton Gwamna Uba Sani yana jawabi a wajen taron APC Hoto: Senator Uba Sani
Source: Facebook

Hakazalika, Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa bindigogi kadai ba za su iya kawo karshen matsalar rashin tsaro ba.

Sai dai wannan martanin ya zo ne ’yan kwanaki bayan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i, ya soki shirin tattaunawa da ’yan bindiga.

Karanta wasu labaran kan 'yan bindiga

Musulman Kudancin Kaduna sun yi korafi

A wani labarin kuma, kun ji cewa Musulman Kudancin Kaduma sun koka kan yadda ake kawo rarrabuwar kawuna a yankin.

Musulman karkashin kungiyar Concerned Muslim Ummah, ta bayyana cewa wasu manyan mutanen yankin suna raba kawuna jama'a ta hanyar amfani da tarihi da siyasa.

Kungiyar ta kuma karyata ikirarin da ake yi na cewa yankin Kudancin Kaduna, na da mutane Kiristoci ne kawai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng