Za a Iya Samun Matsala kan Wadatar Fetur, Dillalan Mai Sun Taso Dangote a Gaba

Za a Iya Samun Matsala kan Wadatar Fetur, Dillalan Mai Sun Taso Dangote a Gaba

  • Kungiyar PETROAN ta sanar da dakatar da daukowa da rarraba man fetur na kwana uku a Najeriya baki daya
  • Matakin kamar yadda aka tabbatar zai fara aiki daga 9 ga Satumbar 2025 don adawa da danniya a kasuwar man fetur
  • Shugaban PETROAN Billy Gillis-Harry ya ce matakin na lumana ne, domin kare hakkin ma’aikata

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Kungiyar masu gidajen man fetur PETROAN ta sanar da shirin dakatar da daukowa da rarraba man fetur a fadin Najeriya.

Kungitar ta ce za ta kawo tsaiko na kwana uku daga 9 ga Satumbar 2025 saboda shirin attajiri Aliko Dangote wanda suke ganin babu adalci.

Yan kasuwa sun taso Dangote a gaba
Gidan man kamfanin NNPCL da Attajiri a Najeriya, Alhaji Aliko Dangote. Hoto: NNPC Limited.
Source: Getty Images

Yan kasuwa sun taso Dangote a gaba

Matakin ya biyo bayan sanarwar NUPENG cewa ma’aikata za su daina aiki daga 8 ga watan Satumba saboda batun rarraba mai na Dangote, cewar TheCable.

Kara karanta wannan

Trump: Amurka ta sake fitar da gargadi game da rashin tsaro a Najeriya

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

PETROAN ta fitar da sanarwa ranar Asabar da Joseph Obele ya rattabawa hannu, inda ta ce dakatarwar za ta fara daga safiyar Talata.

Ta ce:

“Kungiyar PETROAN ta bayyana cewa za ta dakatar da daukowa da rarraba man fetur na kwana uku daga 9 ga Satumba 2025 domin adawa da danniya.”
An fara kai ruwa rana tsakanin yan kasuwa da Dangote
Shugaban kamfanin Dangote a Najeriya, Aliko Dangote da gidan man NNPCL. Hoto: Dangote Foundation.
Source: Facebook

Musabbabin shirin kawo cikas ga rarraba fetur

Shugaban PETROAN na kasa, Billy Gillis-Harry, ya ce za a dauki matakin ne don yin adalci a fannin rarraba mai da kuma adawa da danniya a kasuwa.

Ya bayyana matakin a matsayin “na doka da lumana”, yana mai cewa hakan na nuna jajircewar PETROAN wajen kare ma’aikata da farashin mai da ‘yan Najeriya.

Gillis-Harry ya roki shugaban kasa Bola Tinubu, ministan mai, shugabannin NNPC, NMDPRA, DSS, da IGP su dauki mataki don kauce wa matsaloli.

Ya ce ma’aikatan gidajen man PETROAN suna karkashin NUPENG, wanda suma sun yi barazanar yajin aiki, don haka ba za a hukunta wadanda suka kauracewa aiki ba, Punch ta tabbatar.

Kara karanta wannan

Ba imani: Mahaifiya ta daure jaririyar da ta haifa ta birne ta da rai a dajin Kebbi

A bangaren kasuwa, Gillis-Harry ya soki dabarun kasuwanci na Dangote, yana mai cewa hakan na iya rusa ‘yan kasuwa da direbobin mota.

Ya gargadi ‘yan Najeriya kada su ruɗu da ragin farashi na wucin gadi, saboda danniya na iya haddasa rashin aikin yi da tasirin tattalin arziki.

PETROAN ta ce tana ci gaba da tattaunawa a Lahadi da Litinin, amma za ta ci gaba da shirin idan ba a samu mafita ba.

Kungiyar dillalan mai ta kara da cewa ta kafa kwamitin mutum 120 domin sa ido a gidajen mai da kuma kare kadarori yayin wannan mataki

Dangote, yan kasuwa sun fitar da farashi

Mun ba ku labarin cewa kamfanonin Dangote, Aiteo da AA Rano sun daidaita farashin litar man fetur daga N821 zuwa N823 a Najeriya.

Masana sun bayyana cewa wannan sauyi ya samo asali ne daga hauhawar farashin danyen mai a kasuwar duniya wanda ake da tasiri a farashin mai.

Rahotanni sun nuna cewa farashin gidajen mai bai sauya ba tukuna, amma ana iya ganin karin farashi a yan kwanakin nan masu zuwa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.