'Ku Ji da Kyau': Yahaya Bello Ya ba Ƴan Majalisun Kogi Umarni game da Gwamna Ododo

'Ku Ji da Kyau': Yahaya Bello Ya ba Ƴan Majalisun Kogi Umarni game da Gwamna Ododo

  • An yaɗa wani faifan bidiyo da aka gano tsohon gwamnan Kogi, Yahaya Bello, yana ba yan majalisar dokokin jiharsa umarni
  • Yahaya Bello ya bukaci 'yan majalisar dokoki su mara wa Gwamna Usman Ododo baya, domin ci gaban jihar gaba ɗaya
  • A bidiyon da ke yawo a kafafen sada zumunta, Bello ya umarci manyan mutanen su zauna ƙasa, hakan ya jawo sukar jama'a

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Lokoja, Kogi - Wani bidiyon tsohon gwamnan Kogi da yan majalisu ya jawo maganganu a kafofin sadarwa.

An gano tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello yana ba mambobin majalisar umarni a wata ganawa da aka yi a gidansa da ke jihar Kogi.

Yahaya Bello ya umarci yan majalisa su ba Ododo goyon baya
Yahaya Bello ya bukaci ƴan majalisun Kogi su ba gwamna Ododo goyon baya. Hoto: Yahaya Bello.
Source: Facebook

A bidiyon da Daily Trust ta yada, Yahaya Bello ya bukaci mambobin majalisar dokoki na jihar da su mara wa gwamnatin Gwamna Usman Ododo baya.

Kara karanta wannan

Fadar shugaban kasa ta ragargaji Atiku, El Rufa'i kan wata nasarar da Tinubu ya samu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An taso Yahaya Bello bayan barin gwamna

Bello, ya mika mulki ne ga Ahmed Usman Ododo bayan kammala wa’adinsa a watan Janairu 2024, wanda ya gaje shi domin ci gaba da mulkin jihar.

Tun bayan mika mulki ga Gwamna Ododo, an fara maganar tuhume-tuhume da ake yi kan Yahaya Bello na zargin badakalar makudan kudi.

Hukumar yaki da cin hanci ne ta EFCC fara tuhumar tsohon gwamnan kan zargin almundahana fiye da N80bn yayin da yake mulkin jihar.

Umarnin da Yahaya Bello ya ba yan majalisa

A cikin jawabin nasa ga ‘yan majalisar, tsohon gwamnan ya umarce su da su zauna a kasa, inda ya bukaci haɗin kansu a jihar.

Ya yi kira gare su da su yi aiki tare da Kakakin majalisar, Aliyu Umar Yusuf, da sauran mambobi wajen tallafa wa Gwamna Ododo.

Tsohon gwamnan ya jaddada bukatar majalisar ta goyi bayan duk wasu kudurori da gwamnatin Ododo za ta kawo gaban majalisar jihar Kogi.

Kara karanta wannan

Bayan dawowa daga London, Ganduje ya bi sawun Shettima da Zulum wajen ta'aziyya Kogi

Ya ce:

“Zauna a ƙasa, Don haka, yanzu da za ku shiga... Ku je ku ba da haɗin kai da Kakakin majalisar da sauran mambobi ku tallafa.
“Ku kasance cikin waɗanda za su goyi bayan Gwamna Ahmed Usman Ododo a duk abin da ya zo gaban majalisar."
Yahaya Bello ya ba yan majalisa umarni game da Ododo
Tsohon gwamna, Yahaya Bello yana da kyakkyawar alaƙa da Usman Ododo. Hoto: Yahaya Bello, Alhaji Ahmed Usman Ododo.
Source: Twitter

Alakar da ke tsakanin Yahaya Bello, Ododo

Bayan wannan jawabi nasa, ‘yan majalisar sun yi tafi cikin murna a matsayin martani da godiya ga tsohon gwamnan bayan kammala jawabin nasa.

Hakan ya kara tabbatar da irin alaka mai kyau tsakanin Yahaya Bello da Gwamna Ahmed Usman Ododo a jihar wanda ba kasafai hakan ke faruwa ba.

Yahaya Bello ya auri mata ta 4

Mun ba ku labarin cewa an tabbatar da cewa tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya angwance a bikin da aka gudanar a birnin tarayya, Abuja.

Yahaya Bello ya angwance ne a karo na hudu a Abuja da matarsa, Hiqma a wani bikin sirri da danginsa da abokai suka halarta wanda aka yi.

Matarsa ta uku, Hafiza, ta tabbatar da auren a kafar sadarwa, inda ta yi maraba da sabuwar amarya tare da addu’ar albarka da zaman lafiya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.