Ana cikin Yaɗa Jita Jitar ba Shi da Lafiya, Tinubu Zai Bar Najeriya Gobe Alhamis

Ana cikin Yaɗa Jita Jitar ba Shi da Lafiya, Tinubu Zai Bar Najeriya Gobe Alhamis

  • Shugaba Bola Tinubu zai tashi daga Abuja ranar Alhamis 14 ga watan Agustan 2025 domin halartar wasu taruka a ƙasashe duniya
  • Haminsa a ɓangaren yada labarai ya tabbatar da cewa shugaban zai tafi Japan da Brazil, inda zai halarci taro da ganawa da shugabanni
  • A Japan, zai halarci taron TICAD9 mai taken "Co-create Innovative Solutions with Africa" domin inganta tattalin arziki da jari-hujja

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

FCT, Abuja - Ana tsaka da yada rade-radi cewa ba shi da lafiya, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu zai bar Najeriya.

Bola Tinubu zai bar Abuja ranar Alhamis, 14 ga Agustan 2025 zuwa kasashen Japan da Brazil bayan ya tsaya a Dubai.

Tinubu zai bar Najeriya gobe Alhamis
Tinubu zai tafi kasashen Japan da Brazil. Hoto: @aonanuga1956.
Asali: Twitter

Bola Tinubu zai bar Najeriya ranar Alhamis

Kara karanta wannan

Magana ta kare, bidiyon Shugaba Tinubu ya bayyana ana tsaka da jita jitar ba shi da lafiya

Hadiminsa na musamman a bangaren sadarwa, Bayo Onanuga shi ya tabbatar da haka a shafin X a yammacin yau Laraba 13 ga watan Agustan 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar ta ce Tinubu zai kuma tsaya a birnin Dubai, Hadaddiyar Daular Larabawa kafin ci gaba da tafiya zuwa Japan.

A Japan, Tinubu zai halarci Taron Tokyo karo na tara kan cigaban Afrika (TICAD9) a birnin Yokohama daga 20 zuwa 22 ga watan Agustan 2025.

Taken taron na bana shi ne "Co-create Innovative Solutions with Africa", wanda zai mayar da hankali kan bunkasa tattalin arzikin Afrika ta hanyar jari-hujja da kirkire-kirkire.

Tarukan da Tinubu zai halarta a kasashen duniya

Haka kuma, zai halarci zaman taruka, ya gana da shugabanni, da kuma kamfanonin Japan masu zuba hannun jari a Najeriya don kara hadin kai.

An fara taron TICAD ne a shekarar 1993 da gwamnatin Japan tare da hadin gwiwar Majalisar Dinkin Duniya, UNDP, kungiyar Afrika, da Bankin Duniya.

Kara karanta wannan

'Za mu more': An faɗi dalilai da ke nuna Jonathan ne mafi dacewa da bukatun Arewa

Taron na gudana duk bayan shekaru uku a Japan ko cikin kasashen Afrika, inda na baya ya kasance a Tunisia a watan Agustan 2022.

Tinubu zai shilla kasashen duniya a gobe
Tinubu zai bar Najeriya zuwa kasashen Brazil da Japan. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

Shugaban Brazil ya tura gayyata ga Tinubu

Bayan kammala taron TICAD9, Tinubu zai tafi birnin Brasilia a Brazil, don ziyarar aiki daga ranar Lahadi 24 zuwa Litinin 25 ga watan Agustan 2025.

Ziyarar ta biyo bayan gayyatar shugaban Brazil, Luiz Inacio Lula da Silva, inda za su yi ganawar bangarori biyu da tattaunawa kan harkokin kasuwanci.

Shugaban Najeriya zai kuma halarci taron kasuwanci da ‘yan kasuwar Brazil da kuma rattaba yarjejeniyoyi da fahimtar juna tsakanin kasashen biyu.

Za a samu ministoci da manyan jami’an gwamnati cikin tawagar shugaban, kamar yadda Bayo Onanuga ya bayyana.

Tinubu ya jagoranci taron majalisar zartarwa

Kun ji cewa hadimin shugaban kasa, Abdul'aziz Abdul'aziz ya fitar da faifan bidiyon da ke nuna Bola Tinubu a dakin taron Majalisar Zartarwa (FEC).

Kara karanta wannan

Me ake kullawa: Na hannun daman Kwankwaso ya sake ganawa da Shugaba Tinubu

Hakan ya biyo bayan jita-jitar da ke ci gaba da yawo kan lafiyar shugaban kasa wanda ta zo karshe da bidiyon Shugaba Tinubu ya bayyana a yau Laraba 12 ga watan Agustan 2025.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, sakataren gwamnatin tarayya, George Akume na cikin wadanda suka halarci taron a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.