Matasa Sama da 100,000 Za Su Amfana a Sabon Shirin da Aka Kaddamar a Bauchi

Matasa Sama da 100,000 Za Su Amfana a Sabon Shirin da Aka Kaddamar a Bauchi

  • Gwamnan Bauchi, Sanata Bala Mohammed ya kaddamar da wani sabon shirin ba da horo a fannoni daban-daban na fasahar zamani
  • Shirin, wanda gwamnatin Bauchi ta yi hadin gwiwa da hukumar NITDA zai amfanar da matasa akalla 100,000 ta hanyar ba su horo daga nan zuwa 2027
  • Gwamna Bala ya bayyana cewa shirin zai ba matasa damar gogewa a harkar fasahar zamani, wanda za su samu ayyukan yi a duniya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Bauchi - A yunƙurin ganin Bauchi ta zama cibiyar kirkire-kirkire da fasaha na zamani, Gwamna Bala Mohammed, ya kaddamar da shirin Cybernations, wani tsari na horaswa kan tsaron yanar gizo.

Wannan shiri, wanda aka fi sani da aka fi sani da Digital Literacy and Skill Framework Bauchi Initiative, an ƙirƙire shi ne tare da haɗin gwiwar Hukumar Ci gaban Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA).

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya yi ruwan mukamai a hukumomin tarayya ana jita jitar ciwo

Gwamna Bala tare da matasa a Bauchi.
Gwamnan Bauchi ya kaddamar da shirin bai wa matasa horo kan fasahar zamani Hoto: @SenBalaMohammed
Source: Twitter

Gwamna Bala ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X tare da hotunan kaddamar da shirin a ranar Talata.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shirin zai ba matasa akalla 100,000 horo

Ana sa ran wannan sabon shiri zai ba da horo na ƙwarewar zamani a fannoni daban-daban ga matasa sama 100,000 kafin shekarar 2027.

Da yake jawabi a wajen kaddamarwar a Bauchi, Gwamna Bala Mohammed ya ce wannan shiri “na nuna sabon babi a makomar tattalin arzikin jiharmu."

A cewarsa, shirin zai tabbatar da cewa ’yan ƙasa, musamman matasa, sun samu gogewa da damar shiga harkokin tattalin arzikin zamani na duniya.

Ya ƙara da cewa, shirin mai suna DL4ALL a takaice zai samar da ilimin zamani a makarantu da ma’aikatu, tare da samar da hazikan ma’aikata ga masu ɗaukar aiki na cikin gida da ƙetare.

Yadda matasan Bauchi za su amfana da shirin

Kara karanta wannan

'Yan sandan Kano sun fara binciken kisan 'ɗan fashi' bayan koken uwarsa

Ya kuma bayyana cewa za a ba matasa 2,000 horo na musamman a fannonin fasaha da aka fi buƙata irin su ƙirƙirar manhaja, fasahar AI, tsaron yanar gizo, da sauransu.

“Mun gane cewa fasahar sadarwa a yau da nan gaba ita ce ke habaka cikin sauri, kuma tana da ƙarfin ɗaukar matasa masu ƙwarewa.
"Amfaninta shi ne mutum zai iya samun horo, ya samu takardar shaidar ƙwarewa, sannan ya dogara da ita wajen samun halal.
“Manufarmu a bayyane take, muna son sauya Bauchi zuwa jihar zamani, mai bunƙasar tattalin arziki, kuma mai ƙarfafa kirkire-kirkire.
Muna son amfani da fasaha ba a wajen aiki kadai ba, har da zama silar bunkasa tattalin arziki, ci gaban ɗan adam, da sauyin zamantakewa.”

- Gwamna Bala Muhammed.

Gwamnan Bauchi, Bala Mohammed.
Gwamnan Bauchi na kokarin bai wa mataaa horo a fasahar zamani Hoto: Sen. Bala Mohammed
Source: Twitter

A nasa bangaren, Manajan Darakta na kamfanin Galaxy Backbone, Farfesa Ibrahim Adeyanju, ya jaddada muhimmancin sanin dabarun tsaron yanar gizo a wannan zamani na fasaha.

Ya bayyana buƙatar haɗin kai don bai wa ’yan Najeriya ilimi da kayan aiki da za su ba su damar yin fice a duniyar zamani.

Daukar aiki: Kasashe za su hada kai da Najeriya

Kara karanta wannan

Ana batun yunwa, gwamnatin Tinubu ta fitar da ton 42,000 na hatsi a raba wa jihohi

A wani labarin, kun ji cewa gwamnatin tarayya za ta hada kai da wasu kasashen duniya domin samar sa ayyukan yi ga 'yan Najeriya.

Wannan shiri na daga cikin tsare-tsaren gwamnati na magance matsalar rashin aikin yi da zaman kashe wando tsakanin matasa.

Kasashen da gwamnatin ta ce ta fara tattaunawa da su don samar da ayyuka ga matasa sun hada da Saudiyya, Amurka da sauransu.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262