An Tara Gima Giman Malamai a Kaduna, Sun Bada Fatawa kan Tazarar Haihuwa a Musulunci
- Manyan malamai a Kaduna sun bayyana cewa ya halatta ma'aurata su bayar da tazarar haihuwar yara domin kula da lafiyar mata
- Sun bayyana hakan ne a wurin wani taron kwana ɗaya da ƙungiyar DKT Nigeria International ta shirya a Kaduna
- A cewar malaman, Musulunci ya koyar da ba da tazarar haihuwa saboda lafiyar yara da mata, suka kafa hujjoji da ayoyi da Hadisai
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kaduna - Manyan Malaman Addinin Musulunci a Jihar Kaduna sun bayar da fatawar cewa ya halatta ma'aurata su rika bada tazara tsakanin haihuwar yara.
A cewar malaman, addinin Musulunci ya amince da hakan tare da bayyana amfaninsa ga lafiyar mata da yara.

Source: Original
Daily Trust ta ce an bayyana hakan ne a wani taron wayar da kai na yini daya da aka shiryawa malamai da limamai, wanda ƙungiyar DKT Nigeria International ta dauki nauyi.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Taron ya duba koyarwar addinin musulunci da ilimin lafiya kan batun tazarar haihuwa ta hanyar tattaunawa da manyan malamai masu tasiri a cikin al’umma.
Malaman Kaduna sun yarda da tazarar haihuwa
A lokacin da yake jawabi a taron, Dr. Yakubu Arrigasiyyu, malami daga Majalisar Malamai ya jaddada cewa Musulunci bai haramta bayar da tazarar haihuwa ba.
“Mun yi bincike da nazari game da batun tazara tsakanin haihuwa, musamman daga mahangar addinin Musulunci.
"Akwai Hadisai da ayoyin Alkur’ani da ke nuna yadda Musulunci ke goyon bayan iyaye wajen tsara lokacin da suka dace su haifi yara.”
- Dr. Yakubu Arrigasiyyu.
Gudummuwar da ya kamata malami su bayar
Ya kara da cewa malamai suna taka rawar gani wajen fahimtar da al'umma da koyar da su ilimin da ya kamata su sani dangane da lafiyarsu.
"Malaman Musulunci shugabanni ne, su ne ke jagorantar mutane kuma su koya musu abin da ya dace da abin da bai dace ba.

Kara karanta wannan
Amnesty Int'l ta dura kan Tinubu da gwamnati ta ƙi tsoma baki shekaru 6 da 'sace' Dadiyata
"Idan suka fahimci alherin abu da abinda ya dace, to su ma za su iya yada wannan ilimi zuwa ga mabiyansu," inji shi.
Dr. Yakubu ya roki malamai su isar da wannan saƙo mai muhimmanci game da bada tazarar haihuwa domin kula da lafiyar yara da mata.
Dalilin da ya sa DKT ta shirya taron
A nata bangaren, Husseina Dada, ɗaya daga cikin jagororin ƙungiyar DKT Nigeria International, ta ce sun zaɓi ganawa da malamai ne saboda yadda al'umma suka yarda da su.
"Mu fahimci cewa malamai ya kamata mu fara tattaunawa da su kan batun tazarar haihuwa. Ba da tazara tsakanin yara abu ne mai matukar muhimmanci ga kowace matar aure.
"Mahaifa tana bukatar hutu. Wannan yana ba mata damar farfadowa da kuma ciyar da jaririnsu da abinci mai gina jiki.”
Ta kara da cewa tsarin tazara yana bai wa mata damar kula da gida, sana’a da lafiyarsu yadda ya kamata.
Sarkin Musulmi ya halarci taro a Ingila
A wani rahoton, kun ji cewa Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Sa’ad Abubakar III, ya halarci taron shugabannin Musulmi na duniya a Oxford da ke ƙasar Ingila.

Kara karanta wannan
Ta fara tsami tsakanin ministan Tinubu da Gwamna, an ci gyaran Bago kan matakinsa
Sultan ya bukaci shugabanni da al’umma su rungumi zaman lafiya a matsayin hanyar samun hadin kai da zaman lafiya a duniya.
Ya ƙara da cewa addinin Musulunci na koyar da zaman lafiya, don haka ya kamata a ci gaba da amfani da koyarwar Musulunci wajen tabbatar da fahimtar juna.
Asali: Legit.ng
