Rashin Tsaro: Gwamnatin Katsina Ta Waiwayi Manyan Asibitocin Jihar

Rashin Tsaro: Gwamnatin Katsina Ta Waiwayi Manyan Asibitocin Jihar

  • Gwamnatin jihar Katsina ta dauki damarar samar da tsaro a manyan asibitoci domin kare rayukan ma'aikata da masu jinya
  • A yayin taron majalisar zartarwa, gwamnatin ta amince da kashe N703m don gina katangu a wasu manyan asibitoci na kananan hukumomin da ke da barazanar tsaro
  • Wannan yunkurin dai na zuwa ne yayin da wasu kananan hukumomin jihar ke ci gaba da fuskantar barazanar hare-hare daga 'yan bindiga

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Katsina - Gwamnatin jihar Katsina ta amince da kashe Naira miliyan 703 domin sake gina katangu da kuma sanya shingen tsaro a manyan asibitoci.

Gwamnatin ta amince a yi aikin ne a manyan asibitoci guda 14 da ke wasu kananan hukumomin jihar masu fama da rashin tsaro.

Gwamnatin Katsina za ta gina katangu a asibitoci
Gwamnatin Katsina na son samar da tsaro a asibitoci Hoto: Ibrahima Kaulaha Mohammed
Source: Facebook

Kwamishinan ayyuka, gidaje da sufuri, Dakta Sani Magaji-Ingawa, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a garin Katsina, cewar rahoton jaridar Vanguard.

Kara karanta wannan

Babu dadi: 'Yan bindiga sun yi awon gaba da mata yayin wani hari a Zamfara

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya bayyana hakan ne yayin da yake yi wa manema labarai bayani bayan taron majalisar zartarwa ta jihar.

A ina za a gina katangun?

Sani Magaji-Ingawa ya bayyana cewa, kananan hukumomin da abin ya shafa sun haɗa da Kankara, Malumfashi, Faskari, Jibia da Funtua.

Sauran su ne Kafur, Dandume, Musawa, Batsari, Dutsin-ma, Kurfi, Danmusa, birnin Katsina, da kuma babban asibitin Amadi Rimi.

"Wannan aikin inganta gine-ginen wani ɓangare ne na shirin da gwamnatinmu ke aiwatarwa domin ƙarfafa cibiyoyin lafiya a yankunan da ke fama da matsalolin tsaro, da kuma tabbatar da tsaron ma’aikata da marasa lafiya."

- Sani Magaji-Ingawa

Kwamishinan ya ƙara da cewa, majalisar zartarwa ta amince da ɗaukaka cibiyar lafiya ta Mai’adua zuwa cikakken babban asibiti, a kan kuɗin da ya kai Naira biliyan 1.3.

Haka zalika, Sani Magaji-Ingawa ya bayyana cewa majalisar ta kuma amince da kashe Naira biliyan 18.5 domin gina muhimmin titin Rafin Iya–Tashar Bawa–Sabuwa, rahoton TVC News ya tabbatar.

Kara karanta wannan

Gwara Haka: Jagororin 'yan bindiga sun gwavza fada a Zamfara, an samu asarar rayuka

Ya ce da zarar an kammala aikin, titin zai inganta ayyukan tsaro, sauƙaƙa jigilar kayan noma, da kuma ƙarfafa harkokin kasuwanci da tattalin arziki a yankunan da ya ratsa.

"Muna ɗaukar matakai domin haɗa al’ummomi, tallafawa manoma, da faɗaɗa hanyoyin cikin gida na jiharmu domin samun ci gaba mai ɗorewa".

- Sani Magaji-Ingawa

Gwamnatin Katsina za ta gyara asibitoci
Gwamnatin Katsina za ta gina katangu a wasu asibitoci Hoto: Ibrahima Kaulaha Mohammed
Source: Facebook

Aikin zai taimaka

Ibrahim Kabir ya shaidawa Legit Hausa cewa sake gina katangu a asibitocin zai taimaka sosai wajen samar da tsaro.

"Eh gaskiya ina ganin idan aka yi aikin zai taimaka sosai kan wajen samar da tsaro. Dama bai kamata a ce an bar asibitoci babu katangu ba."
"Muna fatan Allah ya kawo mana karshen wadannan matsalolin."

- Ibrahim Kabir

Karanta wasu labaran kan rashin tsaro a Katsina

An sallami gwamnan Katsina daga asibiti

A wani labarin kuma, kun ji cewa likitoci sun sallami gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda daga asibiti bayan ya yi jinya.

Kara karanta wannan

Tinubu ya amince da kashe sama da N712bn a yi wa filin jirgin Legas kwaskwarima

An dai kwantar da gwamnan ne a wani asibiti da ke birnin tarayya Abuja sakamakon hatsarin motar da ya ritsa da shi.

Likitocin da suka duba gwamnan sun ba da tabbacin cewa ya samu cikakkiyar lafiya kuma zai iya komawa bakin aiki.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng