Ba Dadi: 'Yan Bindiga Sun Yi Wa Sojoji Kwanton Bauna, an Samu Asarar Rayuka
- An samu asarar rayuka bayan da 'yan bindiga suka yi wa jami'an tsaro kwanton bauna a jihar Plateau
- Farmakin da 'yan bindigan suka kai kan jami'an tsaron ya yi sanadiyyar rasa rayukan sojoji da 'yan sa-kai a karamar hukumar Wase
- Lamarin da ya auku bayan da jami'an tsaron suka je kai daukin gaggawa bayan sun samu rahoton shirin 'yan bindiga na kai hari
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
Jihar Plateau - 'Yan bindiga sun kashe sojoji biyu da 'yan sa-kai biyu a wani hari a jihar Plateau.
'Yan bindigan sun kashe jami'an tsaron ne a ranar Talata da rana a kusa da Dogon Ruwa, wani kauye da ke cikin gundumar Bashar a ƙaramar hukumar Wase ta jihar Plateau.

Source: Twitter
Wasu mazauna yankin sun shaidawa jaridar Daily Trust cewa 'yan bindigan sun kwashe bindigogi mallakar sojojin da suka kashe.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
'Yan bindiga sun kashe sojoji a Plateau
Sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:00 na rana, a lokacin da sojoji da 'yan sa-kai ke bin sahun ‘yan bindigan da suka yi ƙoƙarin kai hari a yankin.
Sarkin Safiyo, Abdullahi Yakubu, wanda Dogon Ruwa ke ƙarƙashinsa, ya tabbatar da faruwar lamarin.
A yayin da yake Allah wadai da harin, ya ce sojoji da 'yan sa-kam sun fada tarkon ‘yan bindigan ne ba zato ba sammani.
"An samu rahoton cewa ‘yan bindiga na shirin kai hari Dogon Ruwa. Mutane suka gaggauta sanar da jami’an tsaro, wadanda suka tashi da gaggawa zuwa inda aka ce an gan su."
"Amma ba tare da sanin su ba, ‘yan bindigan sun yi kwantan-ɓauna, suka bude musu wuta wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwar sojoji biyu da 'yan sa-kai biyu."
- Abdullahi Yakubu

Source: Original
Ana tsoron an kwashe kayan sojoji
Wani mazaunin yankin mai suna Ibrahim Sale, ya bayyana cewa bayan kashe jami’an tsaron, ‘yan bindigan sun kwashe bindigoginsu da kayan sojoji.

Kara karanta wannan
Sojojin Najeriya sun fafata da ƴan bindiga, an cafke wani baƙon ɗan ta'adda a Yobe
Ibrahim Sale ya ƙara da cewa, faruwar wannan al’amari ya haddasa fargaba da damuwa a tsakanin mazauna Dogon Ruwa da sauran kauyukan da ke makwabtaka da su.
A halin da ake ciki, mai magana da yawun rundunar Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, bai mayar da martani kan saƙon da aka tura masa kan harin ba har zuwa lokacin da ake hada wannan rahoto.
Karanta wasu labaran kan 'yan bindiga
- 'Yan bindiga sun tare hanya, an yi awon gaba da daliban kwaleji
- Yan bindiga sun saɓa alƙawari, sun yanka mutum 38 bayan dafe miliyoyin kuɗin fansa
- Babu sauki: Dakarun sojoji sun hallaka 'yan bindiga masu yawa a Neja
Sojoji sun hallaka 'yan ta'addan Boko Haram
A wani labarin kuma, kun ji cewa dakarun sojoji na rundunar Operation Hadin Kai sun samu nasarar hallaka 'yan ta'addan Boko Haram a Borno.
Sojojin sun hallaka 'yan ta'addan ne bayan sun yi musu kwanton bauna a karamar hukumar Bama.
Hakazalika, jami'an tsaron sun kwato kayayyaki masu yawa da tare da raunata wasu daga cikin 'yan ta'addan.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng
