Bola Tinubu Zai Karɓi Gawar Buhari da Kansa a Katsina, Ya Tura Ministoci 25 Daura

Bola Tinubu Zai Karɓi Gawar Buhari da Kansa a Katsina, Ya Tura Ministoci 25 Daura

  • Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya shirya tafiya Katsina domin karɓar gawar Muhammadu Buhari da kansa a gobe Talata, 15 ga watan Yuli
  • Ministan yaɗa labarai, Muhammed Idris ne ya sanar da hakan, ya ce ana sa ran isowar gawar da karfe 12:00 na tsakar rana a gobe Talata
  • Bayan isowar gawar, an shirya yin faretin girmamawa na sojoji kafin daga bisani a wuce Daura domin yi wa marigayin jana'iza

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Katsina - Shugaba Bola Tinubu zai tafi Katsina ya tarbi gawar tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a ranar Talata, kafin a yi jana’izarsa a Daura.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da kan Jama'a, Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da ya gudanar a Abuja ranar Litinin.

Shugaban kasa, Bola Tinubu zai je jana'iza.
Shugaban ƙasa, Bola Tinubu zai tarbi gawar Muhammadu Buhari da kansa a Katsina Hoto: @OfficialABAT
Source: Twitter

A cewar Muhammed Idris, ana sa ran gawar Buhari wanda ya rasu a wani asibiti da ke Landan ranar Lahadi, zata iso Najeriya da ƙarfe 12:00 na rana gobe Talata, rahoton Punch.

Kara karanta wannan

Kalaman Buhari 12 da suka yi amo a Najeriya kuma za su sa a rika tunawa da shi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bola Tinubu zai tarbi gawar Buhari a Katsina

“Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, zai karɓi gawar tsohon Shugaba Buhari da kansa a Katsina. Bayan isowar gawar, za a gudanar da faretin girmamawa na soji a filin jirgin sama kafin a wuce zuwa Daura.
“Za a gudanar da sallar jana’iza bayan haka, sannan a binne shi a mahaifarsa da ke Daura,” in ji Idris.

Ya ƙara da cewa Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, yanzu haka yana Landan, inda yake jagorantar tawagar gwamnatin tarayya domin kammala duk wasu takardu da shirye-shiryen dawo da gawar gida Najeriya.

Za a buɗe litattafai a ma'aikatu da hukumomi

Ministan ya bayyana cewa a matsayin wani ɓangare na zaman makoki na ƙasa, Shugaba Tinubu ya umurci a buɗe litattafan ta’aziyya a dukkan Ma’aikatun Tarayya da Hukumomi (MDAs).

Ya ƙara da cewa za a kuma buɗe littafin ta’aziyya na musamman a Cibiyar Taro ta Ƙasa da ƙasa ta Bola Ahmed Tinubu da ke Abuja.

Kara karanta wannan

Rasuwar Buhari: Matakin da APC ta dauka don karrama tsohon shugaban kasa

Muhammaed Idris ya kuma bayyana cewa shugabannin ƙasashe da dama na ci gaba da aiko da saƙonnin ta’aziyya, Tribune Nigeria ta rahoto.

Tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari.
Shugaba Tinubu ya tura ministoci zuwa Daura Hoto: @MBuhari
Source: Getty Images

Tinubu ya tura ministoci 25 zuwa Katsina

Domin tabbatar da tsari mai inganci, Mohammed Idris ya ce Shugaba Tinubu ya kafa Kwamitin jana'iza karkashin jagorancin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume.

Kwamitin zai yi aiki tare da Gwamnatin Jihar Katsina da iyalan marigayi Buhari domin tsara dukkan ayyukan da suka shafi jana’iza Muhammadu Buhari.

Ministan ya ce tuni Tinubu ya umarci mambobi 25 na Majalisar Zartarwa ta Tarayya su tafi Katsina domin halartar jana’iza sannan su zauna a Daura har zuwa ranar Laraba don a yi addu'ar 3 da su.

Daurawa ya roki a yafewa Buhari

A wani labarin, kun ji cewa Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya roki ƴan Najeriya su sanya Muhammadu Buhari a addu'o'insu kana su yafe masa kura-kuransa.

Ƴan Najeriya sun bayyana ra'ayoyi mabanbanta kan yafewa Buhari laifin da wataƙila ya aikata lokacin da yake shugabancin Najeriya.

Sheikh Aminu Daurawa ya roƙi ƴan Najeriya su yafewa Marigayi Buhari kura-kuran da wataƙila ya aikata masu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262