Jerin Sunaye: Shugaba Tinubu Ya ba Ministoci 10 Muhimmin Aiki kan Jana'izar Buhari

Jerin Sunaye: Shugaba Tinubu Ya ba Ministoci 10 Muhimmin Aiki kan Jana'izar Buhari

  • Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya naɗa kwamitin ministoci da manyan jami'an gwamnti domin shirya jana'izar Muhammadu Buhari
  • Kwamitin wanda ya ƙunshi ministoci 10, NSA da ƙunsoshin gwamnati zai yi aiki ne ƙarƙashin sakataren gwamnatin tarayya, George Akume
  • Tinubu ya kuma umarci duka ma'aikatu da hukumomin gwamnati su buɗe littafin ta'aziyya domin jajen rasuwar Buhari

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, GCFR, ya amince da ƙirƙirar Kwamitin Jana'izar marigayi tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari.

Bola Tinubu kafa wannan kwamiti da ya kunshi ministoci 10 domin shiryawa da kuma tsara jana’izar ƙasa ta musamman ga marigayi tsohon Shugaba Muhammadu Buhari, GCFR.

Tinubu ya naɗa kwamitin jana'iza.
Shugaba Tinubu naɗa ministoci 10 da kusoshin gwamnati domin shirya jana'izar Buhari Hoto: @FMINONigeria
Source: Twitter

Hakan dai na kunshe ne a wata sanarwa da ma'aikatar yaɗa labarai da wayar da kan jama'a ta wallafa a shafinta na X yau Litinin, 13 ga watan Yuli, 2025.

Kara karanta wannan

Gwamnonin Arewa 7 su haɗa baki, sun ba da hutun kwana 1 saboda rasuwar Buhari

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu ya ɗora wa kwamitin, wanda Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, CON, zai jagoranta, alhakin tsarawa da gudanar da jana’izar da ta dace da darajar marigayi Buhari.

Ministoci da jiga-jigan kwamitin jana'iza

’Yan kwamitin sun haɗa da:

1. Ministan kuɗi kuma mai Kula da harkokin tattalin arzikin ƙasa, Wale Edun.

2. Ministan kasafin kuɗi da tsare-tsare na tattalin arziki, Atiku Bagudu.

3. Ministan tsaro, Badaru Abubakar.

4. Ministan yaɗa labarai, Mohammed Idris.

5. Ministan ayyuka, Dave Umahi.

6. Ministan harkokin cikin gida, Tunji-Ojo

7. Ministan babban birnin tarayya (FCT), Nyesom Wike

8. Ministan gidaje da raya birane, Arc. Ahmad Ɗangiwa

9. Ƙaramin ministan lafiya.

10. Ministar al’adu da kirƙire-kirkire, Hannatu Musawa.

11. Mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaron, Malam Nuhu Ribaɗu.

12. Mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan tsare-tsare da daidaitawa;

13. Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin siyasa, Kabir Masari.

Kara karanta wannan

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar hutu saboda rasuwar Buhari

14. Sufeto Janar na ’Yan Sanda

15. Darakta Janar na Hukumar DSS;

15. Babban Hafsan Hasoshin Tsaro (CDS).

Ofishin babban sakataren sashen harkokin gwamnati (GSO), zai kasance a matsayin sakatariyar kwamitin.

Marigayi tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari.
Bola Tinubu ya ɗauki matakan karrama Shugaba Buhari Hoto: Muhammadu Buhari
Source: Twitter

Tinubu ya kara ɗaukar matakan karrama Buhari

Domin girmamawa ga Buhari, Shugaba Tinubu ya umarci dukkan Ma’aikatu da Hukumomin Gwamnati (MDAs) su buɗe litattafan ta’aziyya a ƙofofin ofisoshinsu domin bai wa jama’a damar yin jaje.

Bugu da ƙari, za a buɗe babban littafin ta’aziyya ga jakadun ƙasashen waje da sauran jama’a a Ma’aikatar Harkokin Waje da babban ɗakin taron Bola Ahmed Tinubu, Abuja.

Buhari: Darasi 1 da shugabanni za su ɗauka

A wani labarin, kun ji cewa Farouk Aliyu ya bayyana cewa darasi ɗaya da ya kamata shugabanni su ɗauka daga rasuwar Muhammadu Buhari shi ne akwai mutuwa.

Farouk ya ƙara da cewa duk da Buhari na da wasu kurakurai, ya kamata a girmama shi saboda gudummawar da ya bayar wajen ci gaban ƙasa.

Ya nuna damuwa kan yadda wasu ke sukar Buhari da zagi a kafafen sada zumunta, yana mai cewa a yanzu addu'a yake buƙata da kuma.girmamawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262