Atiku, Ganduje, Saraki Barau Sun Taru a Auren Ɗan Tsohon Shugaban Ƙasa a Abuja

Atiku, Ganduje, Saraki Barau Sun Taru a Auren Ɗan Tsohon Shugaban Ƙasa a Abuja

  • Fitattun 'yan Najeriya sun taru a Babban Masallacin Abuja domin shaida daurin auren Musa Yar’Adua da Maryam Ayuba bayan sallar Juma’a
  • Daga cikin manyan baki akwai dangin marigayin shugaban ƙasa Umaru Yar’Adua da sauran abokai da ‘yan siyasa masu mutunci da dangantaka da iyalan
  • An yi addu'a da roƙon Allah ya ba sababbin ma’auratan hikima da haƙuri domin gina gida mai cike da farin ciki da fahimtar juna

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

FCT, Abuja - A yau Juma’a, 11 ga Yuli, manyan baki daga sassa daban-daban na ƙasar nan sun taru a babban masallacin birnin tarayya da ke Abuja.

Hakan ya biyo bayan daura auren auren Musa Umaru Yar’Adua, ɗan marigayi Shugaban Ƙasa, Umaru Musa Yar’Adua, da Amaryarsa, Maryam Ayuba Shuaibu.

Atiku, Ganduje da Saraki sun hadu a wurin daurin aure
Atiku, Ganduje, Saraki sun halarci daurin auren ɗan marigayi Umaru Musa Yar'adua. Hoto: Atiku Abubakar.
Source: Facebook

Manyan jiga-jigai da suka taru a daurin aure

Kara karanta wannan

Babban malami a masallacin Annabi Muhammad SAW ya riga mu gidan gaskiya

Hakan na cikin wata sanarwa da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya wallafa a shafin X a daren yau Juma'a 11 ga watan Yulin 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An gudanar da daurin auren ne bayan kammala Sallar Juma’a, inda aka shaida fitattun mutane daga siyasa, addini da al’adun gargajiya da suka halarta tare da iyalai da abokai.

Atiku na daga cikin manyan bakin da suka halarci daurin auren ya wanda ya bayyana cewa akwai zumunci mai karfi tsakaninsa da iyalan Yar’Adua tun da dadewa.

Atiku da Ganduje sun sake haduwa a daurin aure
Atiku, Ganduje, Saraki sun halarci daurin aure a Abuja. Hoto: Atiku Abubakar.
Source: Depositphotos

Atiku ya yabawa tarbiyyar gidan marigayi Yar'adua

Atiku ya bayyana cewa sababbin ma’auratan sun fito daga gida mai cike da tarbiyya da mutunci, kuma sun gaji ginshikan al’ada da tsantsar addini a rayuwarsu.

Daurin auren ya kasance taron farin ciki da addu’o’i, inda mahalarta suka roƙi Allah ya ba Musa da Maryam haƙuri, hikima da fahimtar juna.

An jaddada cewa wannan aure zai zama tushe na gina gida mai albarka da cike da zaman lafiya da ƙaunar juna a tsakanin ma’auratan.

Manyan baki da suka halarci daurin auren

Sauran wadansa suka halarci daurin auren akwai tsohon shugaban jam'iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje wanda Bola Tinubu ya sake nada shi mukami a gwamnatinsa.

Kara karanta wannan

Littafi: Garba Shehu ya tara Gowon, Atiku, Osinbajo, El Rufa'i, Aminu Ado a Abuja

Sauran wadanda suka halarci daurin auren akwai mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin da tsohon gwamnan Kwara kuma tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata Bukola Saraki.

Har ila yau, akwai manyan yan siyasa da yan kasuwa wadanda suka samu halartar daurin auren domin sanya albarka ga yayan marigayin.

Kwankwaso, El-Rufai da jiga-jigai sun hadu a Abuja

Kun ji cewa tsohon Antoni-Janar na tarayya, Mohammed Bello Adoke ya kaddamar da littafinsa a birnin tarayya Abuja a wannan mako da muke ciki.

Shahararrun ‘yan siyasa da suka halarci taron sun hada da Mataimakin Shugaban kasa, Kashim Shettima, Rabiu Kwankwaso da tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai.

Mohammed A doke ya bayyana cewa ya yafewa duk wanda ke da hannu a shari’ar da ta bata masa suna dangane da OPL245 lokacin mulkin Muhammadu Buhari a Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.