'Yan Bindiga Sun Bude Wuta kan Jami'an Tsaro, an Samu Asarar Rayuka

'Yan Bindiga Sun Bude Wuta kan Jami'an Tsaro, an Samu Asarar Rayuka

  • Wasu ƴan bindiga ɗauke da makamai sun kai farmaki kan jami'an tsaro na hukumar NSCDC a jihar Bayelsa
  • Ƴan bindigan sun farmaki jami'an tsaron ne a ranar Juma'a inda suka hallaka mutum ɗaya tare da lalata wasu da dama
  • Kakakin hukumar NSCDC a jihar Bayelsa ya tabbatar da aukuwar lamarin, wanda ya auku a ƙauyen Igbomotoru

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Bayelsa - Wasu da ake zargin ƴan bindiga ne sun kai hari kan tawagar sintiri ta hukumar tsaron NSCDC a ƙauyen Igbomotoru, cikin ƙaramar hukumar Southern Ijaw ta jihar Bayelsa.

Ƴan bindigan waɗanda suka kai harin a ranar Juma'a, sun kashe wani jami’in hukumar da har yanzu ba a tantance sunansa ba.

'Yan bindiga sun farmaki jami'an NSCDC a Bayelsa
'Yan bindiga sun hallaka jami'in hukumar NSCDC a Bayelsa Hoto: @Official_NSCDC
Asali: Twitter

Wani mazaunin yankin ya tabbatarwa da jaridar Daily Trust aukuwar lamarin kai harin da ƴan bindiga suka yi a kan jami'an tsaron.

Kara karanta wannan

Ana jimamin kisan kusan mutum 50, an sake sabon ta'addanci a Plateau

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda ƴan bindiga suka farmaki jami'an NSCDC

Ya bayyana cewa tawagar ta NSCDC tana kan hanyar dawowa ne daga wani samame da suka kai kan wuraren haƙar mai ba bisa ƙa'ida ba a yankin lokacin da harin ya auku.

Yankin Igbomotoru ya yi ƙaurin suna wajen haƙar mai ba bisa ƙa'ida ba saboda kasancewarsa wajen da ke da yawan rafuka.

Wasu majiyoyi sun bayyana harin a matsayin wani shiri na tsanaki da wasu ƴan bindiga suka yi, inda suka buɗe wuta kan jirgin ruwa na sintirin NSCDC a kusa da Koluama, wanda aka daɗe ana saninsa a matsayin cibiyar satar mai.

Ana kyautata zaton harin yana da nasaba da masu lalata bututun mai, waɗanda suka yi amfani da muggan makamai don korar jami’an tsaro.

An ce jami’in da aka kashe, an harbe shi ne a lokacin musayar wuta, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa, yayin da sauran jami’an da suka jikkata ake ba su kulawa a wani asibiti da ke birnin Yenagoa.

Kara karanta wannan

Jami'an tsaro sun samu gagarumar nasara kan 'yan bindiga a Katsina

Me hukumar NSCDC ta ce kan harin?

Hukumar NSCDC
'Yan bindiga sun kashe jami'in NSCDC a Bayelsa Hoto: @OfficialNSCDC
Asali: Twitter

Da aka tuntuɓi mai magana da yawun NSCDC na jihar Bayelsa, Solomon Ogbere, a ranar Lahadi, ya bayyana cewa har yanzu bai samu cikakken rahoto kan abin da ya faru ba.

"Eh da gaske ne mun samu rahoton faruwar lamarin, amma har yanzu ina jiran OC ya bani cikakken bayani. Amma abin da kuka faɗa akwai gaskiya a cikinsa, sai dai ba zan iya faɗin komai yanzu ba saboda ban samu cikakkun bayanai ba."
"Amma Insha Allahu gobe (Litinin) zan faɗi komai kan abinda ya faru, adadin waɗanda suka rasa rayuka da sauran bayanai."
"To amma dai wani abu makamancin haka ya faru, sai dai har yanzu ban samu cikakken rahoto a kansa ba."

- Solomon Ogbere

Ƴan bindiga sin farmaki ɗaliban jami'a

A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu yan bondiga sun kai hari kan ɗaliban jami'ar tarayya ta Birnin Kebbi (FUBK).

Kara karanta wannan

Rashin imani: 'Yan bindiga sun zo da sabon salon ta'addanci a Katsina

Ƴan bindigan waɗanda ba a san ko su waye ba sun kai harin ne a wani gidan haya da ke wajen harabar jami'ar.

A yayin harin, ƴan bindigan sun yi awon gaba da wani ɗalibi mai suna Stephen Madubiya zuwa cikin daji.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng