'Ƴan Ta'addan Lakurawa Sun Farmaki Jami'an Tsaro a Kebbi, an Rasa Rayuka

'Ƴan Ta'addan Lakurawa Sun Farmaki Jami'an Tsaro a Kebbi, an Rasa Rayuka

  • Jami'an tsaro na ƴan sa-kai sun rasa rayukansu a wani kwanton ɓauna da suna shiryawa ƴan ta'addan Lakurawa a Kebbi
  • Ƴan ta'addan na Lakurawa sun hallaka ƴan sa-kan ne a ranar Lahadi a ƙauyen Morai da ke ƙaramar hukumar Augie
  • Jami'an na ƴan sa-kai sun yi yunƙurin ƙwato shanun da ƴan ta'addan suka sace ne bayan sun kawo farmaki a ƙauyen

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Kebbi - Ƴan ta’addan ƙungiyar Lakurawa sun kashe mutane 13 daga cikin ƴan sa-kai a jihar Kebbi.

Ƴan Lakurawan sun kashe ƴan sa-kan ne a wani hari da da suka kai a ƙauyen Morai da ke ƙaramar hukumar Augie a jihar Kebbi a ranar Lahadi.

'Yan Lakurawa sun kai hari a Kebbi
'Ƴan ta'addan Lakurawa sun kashe 'yan sa-kai a Kebbi Hoto: @HQNigerianArmy, @NasiridrisKG
Asali: Facebook

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa ƴan sa-kan guda 13 sun rasa rayukansu ne lokacin da suka yi yunƙurin daƙile harin da ƴan ta’addan suka kai.

Kara karanta wannan

'Yan ta'adda sun yi tsaurin ido, sun farmaki sakataren gwamnatin Plataeu

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ƴan sa-kan sun yi ƙoƙarin hana ƴan ta'addan tafiya da shanun da suka sace ne bayan sun farmaki ƙauyen.

Yadda ƴan Lakurawa suka kashe ƴan sa-kai

Tashar Channels tv ta ce wani mazaunin yankin, Malam Ibrahim Augie, ya bayyana cewa ƴan sa-kai da dama ne suka fito domin daƙile harin da ƴan ta’addan suka kai bayan samun labarin zuwansu.

Ya ƙara da cewa kafin su kai ga yin wani abu, ƴan ta’addan sun riga sun kewaye su, sannan suka kashe 13 daga cikinsu.

"Ƴan sa-kai sun ɓoye domin kai wa ƴan ta’addan farmaki da kuma ƙwato shanun da aka sace, amma abin takaici shi ne, ba su sani ba cewa sun riga sun hango su. Sai suka buɗe musu wuta, suka kashe su."
"Babban abin takaicin shi ne ba su sani ba cewa ƴan ta'addan sun riga da sun kewaye su."
"Suna motsawa domin tare hanyar ƴan ta’addan, sai kawai maharan suka buɗe musu wuta, inda nan take suka hallaka aƙalla mutane 13. Ƙauyen da abin ya faru yana da nisan kimanin kilomita uku kacal daga ƙauyenmu."

Kara karanta wannan

Dakarun sojoji sun gwabza fada da 'yan Boko Haram, an samu asarar rayuka

- Malam Ibrahim Augie

Ya zuwa yanzu, an samo gawarwaki guda shida daga cikin waɗanda aka kashe, kuma an riga an yi musu jana’iza bisa tsarin addinin Musulunci.

Bayanai sun ce ana kuma ci gaba da bincike don gano sauran gawarwakin da suka ɓace cikin daji.

'Yan Lakurawa sun kai hari a Kebbi
'Ƴan ta'addan Lakurawa sun hallaka 'yan sa-kai 13 a Kebbi Hoto: @ZagazolaMakama
Asali: Twitter

Me ƴan sanda suka ce kan harin Lakurawan?

Kokarin jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na rundunar ƴan sandan jihar Kebbi, CSP Nafiu Abubakar, bai yi nasara ba har zuwa lokacin da ake haɗa wannan rahoto, domin ba a samu wayarsa ba.

Wannan hari na baya-bayan nan ya sake tayar da hankali a tsakanin al’ummomin jihar Kebbi, musamman a yankunan karkara da ke fama da matsalar ƴan bindiga da ƴan ta’adda.

Ƴan ta'adda sun farmaki sakataren gwamnatin Plateau

A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu ƴan ta'adda sun kai farmaki kan sakataren gwamnatin jihar Plateau, Samuel Jatau.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun yi kwanton bauna, sun hallaka 'yan kasar waje da dan sanda

Ƴan ta'addan sun farmaki ayarin motocin sakataren gwamnatin ne lokacin da yake kan hanyar zuwa ƙaramar hukumar Bokkos.

Samuel Jatau ya samu ya tsallake rijiya da baya a harin bayan jami'an tsaron da ke tare da shi sun buɗewa ƴan ta'addan wuta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng

iiq_pixel