Abin da Mazauna Kano Ke Cewa da ’Yan Sanda Suka Gayyaci Sanusi II zuwa Abuja

Abin da Mazauna Kano Ke Cewa da ’Yan Sanda Suka Gayyaci Sanusi II zuwa Abuja

  • Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II zai gana da Sufeto Janar na ‘yan sanda a Abuja ranar Talata
  • An gayyaci Sanusi ne kan wani al’amari da ya faru a lokacin bukukuwan Sallah a Kano
  • Wasu mazauna Kano sun soki wannan gayyata, suna cewa yana da nufin tayar da rikici a jihar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Wasu mazauna Kano sun yi magana kan gayyatar Sarki Sanusi II da yan sanda suka yi zuwa birnin Abuja.

Wasu daga cikinsu sun nuna rashin jin dadinsu kan wannan gayyata, suna ganin wata dabara ce ta kifar da Sarki Sanusi II daga sarauta.

Mazauna sun tsorata da gayyatar Sanusi II da yan sanda suka yi
Wasu mazauna Kano sun nuna damuwa bayan yan sanda sun gayyaci Sanusi II zuwa Abuja. Hoto: Sanusi II Dynasty, Nigeria Police Force.
Asali: Facebook

Takardar gayyatar Sarki Sanusi II zuwa Abuja

Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, zai gana da Sufeto Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun, a babban hedkwatar ‘yan sanda dake Abuja ranar Talata, cewar Punch.

Kara karanta wannan

Bayan rasa rai a bikin sallah, ƴan sanda sun gayyaci Sarki Sanusi II zuwa Abuja

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An gayyaci Sanusi ne ta wasika da aka rubuta a ranar 4 ga watan Afrilu, wadda Kwamishinan ‘yan sanda (Ayyuka), Olajide Ibitoye, ya sanya wa hannu.

A cewar wasikar, an bukaci Sanusi da ya bayyana a hedkwatar sashin leken asirin ‘yan sanda dake Abuja karfe goma na safe.

Yan sanda sun gayyaci Sanusi II zuwa Abuja
Mazauna sun soki shirin gayyatar Sarki Sanusi II zuwa Abuja da yan sanda suka yi. Hoto: Sanusi II Dynasty, Nigeria Police Force.
Asali: UGC

An rasa rai yayin bikin sallah a Kano

Rahotanni sun ce gayyatar na da nasaba da wani lamari da ya faru a lokacin Sallah a Kano, kodayake ‘yan sanda ba su bayyana cikakken bayani ba.

Majiyoyi daban-daban sun tabbatar da cewa hakan yana da alaka da jerin gwanon motoci da aka yi duk da haramta shi daga wajen ‘yan sanda.

An samu rikici da asarar rai sakamakon wannan jerin gwanon da aka gudanar, wanda hakan ya kara tayar da hankali a Kano.

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano ta kama wani Usman Sagiru a ranar 30 ga watan Maris, 2025, bisa zargin kashe wani da hari kan ‘yan sintiri.

Kara karanta wannan

Galadima: Aminu Ado na karbar ta'aziyya a fadarsa, sarakuna, 'yan siyasa na tururuwa

Martanin wasu yan Kano kan gayyatar Sanusi II

Mafi yawan wadanda suka yi magana kan lamarin sun bayyana rashin jin kan abin da suka kira wani shiri na lalata zaman lafiyar Kano.

Suka ce hakan wani shiri ne na neman hanyar sanya dokar ta-baci a jihar kamar yadda aka yi a Rivers da ke Kudancin Najeriya.

Wani mazaunin Kano da ya bukaci boye sunansa ya ce:

“Muna gargadi kan wadannan dabaru na haddasa rikici a Kano domin a samu damar sanya dokar ta baci.”

Har ila yau, wani ya bayyana cewa:

“Abin da ya faru ranar Sallah ba hawa ba ne, sai dai tafiyar Sarkin daga masallaci zuwa fadarsa.”

Mazauna Kano sun yi kira ga ‘yan sanda da kada su lalata zaman lafiya da ke Kano da wata hujja maras karfi da za ta tayar da hankali.

Sanusi II ya yabawa Abba Kabir Yusuf

Kun ji cewa Mai Martaba sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II ya yabawa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa ayyukan ci gaba da yake zuba wa a Kano.

Kara karanta wannan

Sarki Sanusi II ya yi babban rashi, Galadiman Kano, Abbas Sanusi ya rasu

Sanusi II ya ce ƙoƙarin da gwamnan ke yi na inganta harkokin ilimi, kiwon lafiya noma da tsaro a jihar Kano ya cancanci a jinjina masa.

Gwamna Abba Kabir ya jaddada godiya ga mai martaba sarkin bisa jagorancin da yake yi da tabbatar da zaman lafiya da hadin kai a Kano.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.