Lauya Ya Mika Bukatu 7 ga Bola Tinubu da Gwamna kan Kisan Hausawa a Edo
- An bukaci gwamnatoci su fitar da bayani kan yawan mutanen da aka kashe, jikkata ko yi wa asarar dukiya a Edo
- ‘Yan Arewa sun nemi kamawa da hukunta duk masu hannu a kisan gillar da aka yi wa Hausawa matafiya
- An bukaci kafa kwamitin bincike da samar da sabuwar doka domin hana sake faruwar irin wannan lamari nan gaba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Kano - Kungiyoyi da fitattun ‘yan Arewa sun bukaci gaggauta daukar matakan bincike da hukunta wadanda suka kashe Hausawa a Edo.
Rahotanni sun bayyana cewa wasu matasa sun dauki doka a hannunsu, suka hallaka wasu matafiya da ake zargi da dauke da makamai ba tare da sahihin bincike ba.

Asali: Facebook
A wata sanarwa da lauya mai kare hakkin dan Adam, Barista Abba Hikima, ya wallafa a Facebook, an bukaci daukar matakan da suka dace domin tabbatar da adalci.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Bukatar gaggauta bincike da hukunta masu laifi
Sanarwar ta bukaci gwamnati ta fitar da cikakken bayani kan adadin mutanen da aka kashe, jikkata ko yi wa asarar dukiya a jihar Edo.
A cewar sanarwar:
"Gwamnati na da alhakin tabbatar da adalci ta hanyar bincike da hukunta duk wadanda ke da hannu a wannan kisan gilla,"
Haka nan an bukaci kafa kotu ta musamman da za ta gudanar da shari’a cikin gaggawa domin kada lamarin ya shafe kamar yadda aka saba.

Asali: Facebook
Bukatar biyan diyya da tabbatar da tsaro
Sanarwar ta bukaci gwamnati ta biya diyya ga iyalan wadanda aka kashe tare da basu hakuri a hukumance domin kwantar da hankulan jama’a.
A cewarta:
"Dole ne a biya iyalan mamatan diyya tare da basu hakuri a hukumance domin hana yaduwar tashin hankali a tsakanin al’umma."
Baya ga haka, an bukaci samar da karin jami’an tsaro a yankunan Kudu domin kare rayuka da dukiyoyin matafiya daga irin wannan farmaki a nan gaba.
Bukatar sabuwar doka da kwamitin bincike
Sanarwar ta bukaci a samar da sabuwar doka da za ta tsaurara hukunci kan masu daukar doka a hannunsu domin hana irin wannan kisan gilla nan gaba.
Haka nan an bukaci kafa kwamitin bincike na musamman da zai kunshi wakilan Arewa domin tabbatar da cewa ba a shashantar da lamarin ba.
A cewar sanarwar:
"Kafa kwamitin bincike zai tabbatar da cewa ba a bari wannan lamari ya wuce ba, kuma zai hana sake aukuwar irin hakan a nan gaba."
Bukatun 7 da Abba Hikima suka gabatar
Lauya mai kare hakkin dan Adam, Abba Hikima ya lissafa jerin bukatun da ake bukata Bola Tinubu da gwamnatin Edo su yi kan lamarin:

Kara karanta wannan
"Ba yau aka fara ba," Gwamnatin Kano ta yi zazzafan martani kan kisan ƴan Arewa a Edo
1. Gwamnati ta fitar da cikakken bayani kan mutanen da aka kashe, jikkata ko yi wa asarar dukiya a Edo.
2. A gaggauta kama da hukunta duk masu hannu a wannan kisan, musamman 'yan banga
3. A samar da kotu ta musamman don shari’ar wadanda suka aikata kisan gillar.
4. Gwamnati ta biya diyya ga iyalan wadanda aka kashe tare da basu hakuri a hukumance.
5. A kara samar da jami’an tsaro a yankunan kudu domin kare matafiya da direbobi.
6. A samar da sabuwar doka da za ta tsaurara hukunci kan masu daukar doka a hannu.
7. A kafa kwamitin bincike na musamman da zai kunshi wakilan Arewa domin tabbatar da an yi adalci.
An kama wadanda suka kashe Hausawa a Edo
A wani rahoton, kun ji cewa rundunar 'yan sanda ta kama wasu daga cikin wadanda suka kashe 'yan Arewa a jihar Edo.
Sufeton 'yan sanda ya tabbatar da cewa za a yi adalci wajen hukunta duk wanda aka samu da hannu a cikin aikata kisan gillar.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng