"Abin Tausayi": An Ji Ainihin Yadda Aka Kashe Ƴan Arewa a Jihar Edo, Mutum 5 Suka Tsira
- Wani dattijo ɗan asalin jihar Kano, Ɗayyabu Yahaya ya yi bayanin yadda aka tare su a Uromi, aka kashe ƴan uwansa a Edo
- Ɗayyabu na ɗaya daga cikin mafarautan da aka tare a Uromi, inda ake zagin mutanen garin sun kashe 16 daga cikinsu
- Ya ce su 27 suka taso daga Fatakwal za su dawo Kano kuma ba su gamu da wata matsala ba sai da suka shigo jihar Edo
CHECK OUT: Education is Your Right! Don’t Let Social Norms Hold You Back. Learn Online with LEGIT. Enroll Now!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Edo - A jiya Juma'a ne aka samu labarin kisan wasu mafarauta ƴan Arewa da suka taso daga Fatakwal za su dawo gida domin yin shagalin sallah.
Sai dai daga cikin mutanen su 27, akalla mutum biyar ne suka tsira, wasu mutum biyu na kwance a asibiti, yayin da ake zargin an kashe mutane 20 a garin Uromi na jihar Edo.

Kara karanta wannan
Barau ya yi martani kan kisan 'yan Arewa a Edo, ya fadi hanyar da zai samo musu adalci

Asali: Facebook
Menene ainihin abin da ya faru a Edo?
Ɗaya daga cikin wadanda suka tsira daga wannan lamari ya yi bayanin yadda aka kashe ƴan uwansa a wani bidiyo da Yahaya Abubakar ya wallafa a Facebook.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Dattijon da ya bayyana sunansa da Ɗayyabu Yahaya, ya fito ne daga ƙaramar hukumar Bunkure ta jihar Kano, ya ce sun taho ne da nufin zuwa gida su yi sallah.
Da yake ba da labarin haƙiƙanin abin da ya faru, mutumin wanda alamu suka nuna ya na cikin damuwa, ya ce:
"Tun da muka taso daga Fatakwal ba mu samu matsalar komai ba sai da muka zo Uromi, a nan ne ƴan bijilanti suka tare mu. Ni ina gaban mota, sun ce direba ya sauƙo amma bai sauka ba.
"Sai suka ce na sama su sauko, tun da suka fara saukowa suka fara dukansu, suka tara su wuri ɗaya, suka ci gaba da bugunsu a ka."
Da gaske an kama su da bindigogi?
Da aka tambaye shi kan bindigun da aka ce an kama su da su, mutumin ya bayyana cewa babu abin da aka samu sai tsunmokara da manjar da suka sayo.
"Eh sun bincike mu, ƴan bijilanti sun zo da wuƙakensu, suka rika buɗe kayanmu amma ba abin da suka samu daga tsunmokarai sai manja. Da suka ga bindigogin mu na maharba sai suka ce mu ƴan garkuwa ne.
"Taya ɗan garkuwa zai taho tare da kare tun daga Fatakwal zuwa Kano? Bindigogin duk na maharba ne kuma muna da takardu," in ji shi.

Asali: Original
Ƴan Arewa nawa aka kashe a jihar Edo?
Dangane da adadin mutanen da aka kashe kuwa, Ɗayyabu ya ce su 27 ne suka taho a motar amma su biyar ne suka tsira da rayuwarsu.
"Mu 27 ne a motar, ban san mutum nawa aka kashe ba amma mu 5 muka rage a raye, an ce akwai mutum biyu a asibiti."

Kara karanta wannan
"Ba yau aka fara ba," Gwamnatin Kano ta yi zazzafan martani kan kisan ƴan Arewa a Edo
Pantami ya saukaka wa jami'an tsaro aiki
A wani rahoton, kun ji cewa Sheikh Isa Pantami ya yi Allah wadai da kisan matagiya a Edo, ya buƙaci hukumomi su kama dukan masu hannu a lamarin.
Tsohon ministan sadarwa ya jero hanyoyi 3 na fasaha da za a iya amfani da su wajen cafke waɗanda suka yi wannan aika-aika.
Asali: Legit.ng