Gwamna Ya Daina Ɓoye Ɓoye, Ya Jero Mutanen da Ke Jefa Matasa Harkar Ƴan Bindiga

Gwamna Ya Daina Ɓoye Ɓoye, Ya Jero Mutanen da Ke Jefa Matasa Harkar Ƴan Bindiga

  • Gwamna Charles Soludo na jihar Anambra ya gano yadda bokaye da malaman tsibbu ke yaudarar matasa suna shiga harkokin laifi
  • Soludo ya ce gwamnatinsa ta ɗauki matakan shawo kan wannan matsala kuma tuni ta fara bincike kan bokaye da irin waɗannan malamai
  • Cikin laifukan da bokayen ke yaudarar matasa su fara har da safarar miyagun kwayoyi da shiga kungiyoyin ƴan bindiga da garkuwa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Anambra - Gwamnan Jihar Anambra, Charles Soludo, ya caccaki bokaye da malaman tsibbu da ke yaudarar matasa da alkawarin kariya ta sihiri wajen aikata laifuka.

Gwamna Soludo ya ce bokaye ke yaudarar matasa su jefa su cikin aikata miyagun laifuka irin su safarar miyagun kwayoyi, damfarar yanar gizo da garkuwa da mutane.

Gwamna Soludo.
Gwamna Soludo ya gano yadda bokaye ke rura wutar rashin tsaro a Anambra Hoto: Charles Chikwuma Soludo
Source: Facebook

Farfesa Soludo ya fallasa wannan sirrin ne a wata hira da manema labarai a Awka, babban birnin jihar Anambra, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Zargin lalata: Sanata Natasha na tsaka mai wuya, Hadimin Osinbajo ya tona shirin majalisa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda bokaye ke yaudarar matasa

Soludo ya bayyana cewa bokaye na yin mummunan tasiri a rayuwar matasa, suke ba su tabbacin cewa za su tsira daga doka ta hanyar amfani da asiri da layu.

Ya ce hakan ya jefa dubban matasan Najeriya cikin mawuyacin hali, yayin da da-dama ke fuskantar dauri a gidajen yari na kasashen waje.

Gwamna Soludo ya ce:

“Ana yi wa matasa asirin Oke-Ite don yaudararsu cewa za su iya wuce wuraren bincike ba tare da an gano su da miyagun kwayoyi ba.
"Amma da zarar an kama su, sai su kare a gidan yari. Idan hakan ya kasa, sai su juya zuwa damfara ta yanar gizo, idan hakan ma bai yi nasara ba, sai su fada harkar ƴan bindiga/garkuwa da mutane domin samun kudi cikin sauki."

Wasu matakai Gwamna Soludo ya ɗauka

Gwamna Soludo ya ƙara da cewa gwamnatinsa ta fara ɗaukar matakan tsaftace Anambra daga irin wadannan miyagun ayyuka na bokaye da malaman tsibbu.

Kara karanta wannan

Mataimakiyar gwamna ta ji wuta, ta yi murabus daga muƙaminta? Bayanai sun fito

Ya ce a halin yanzu an fara gudanar da bincike kan bokaye da wasu malamai fiye da 30 da ake zargi da hannu a aikata miyagun laifuka.

Ya kara da cewa, tun bayan fara wannan bincike, da dama daga cikin bokayen sun tsere daga jihar, yayin da wasu ke fargabar cewa sihirinsu zai daina aiki saboda kama shugabanninsu.

Gwamnatin Anambra ta fara gano abubuwa

Gwamnan ya ce an kwato tukwane da dama na Oke-Ite kuma za a yi musu gwajin binciken kimiyya.

Ya ce idan aka gano cewa akwai jinin dan Adam a cikin wadannan tukwane, masu su za su fuskanci hukunci mai tsanani.

Gwamna Soludo.
Gwamnatin Anambra ya taso bokaye da malaman tsibbu Hoto: Charles Chikwuma Soludo
Source: Facebook

Soludo ya jaddada cewa burinsa shi ne ya mayar da Anambra cibiyar kasuwanci da masana’antu, inda mutane za su iya rayuwa cikin kwanciyar hankali.

Ya bukaci kowa, ba tare da la’akari da kabila ko addini ba, da ya hada hannu da gwamnatinsa don tabbatar da zaman lafiya da ci gaban jihar.

Gwamnatin Anambra ta rusa otal

Ku na da labarin cewa gwamnatin jihar Anambra karkashin Gwamna Soludo ta rusa wani otel wanda aka bayyana a matsayin maboyar masu garkuwa da mutane.

Kara karanta wannan

Makusancin Kwankwaso, Buba Galadima ya hango illar saukar farashin abinci

Rahotanni sun nuna cewa an gano kaburbura sama da 30 da aka tsara a wani sashe na ginin, tare da wajen tsafi da ake amfani da shi wajen aikata miyagun ayyuka.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262