Boko Haram Ta Tsallaka, Ta Kai Harin Ramuwar Gayya a Neja, Ta Kashe Bayin Allah

Boko Haram Ta Tsallaka, Ta Kai Harin Ramuwar Gayya a Neja, Ta Kashe Bayin Allah

  • Mayakan Boko Haram sun kai wani mummunan hari da ake zaton na ramuwar gayya ne a ƙauyen Karaga da ke Jihar Neja
  • Rahotanni sun bayyana cewa ana kyautata zaton harin na ramuwar gayya ne bayan jami'an tsaro sun yi wa kungiyar Boko Haram illa
  • A watan Oktoba ne aka hallaka manyan dakarun Boko Haram guda biyar, ciki har da wani ƙwararre a harkar abubuwa masu fashewa
  • A harin da ta kai a matsayin martani, kungiyar ta hallaka maza kacokan, yayin da ta bar mata da yara da ba su haura shekaru 12 ba

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Niger - Akalla mutum 11 ne suka rasa rayukansu a wani mummunan hari da ake zargin ‘yan Boko Haram sun kai a wajen hakar zinariya da ke ƙauyen Karaga, a jihar Neja.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kashe mutane 10, sun sace ɗaliban jami'a 4 a wasu jihohin Arewa

Rahotanni sun bayyana cewa wurin hakar ma'adinan yana kusa da mafakar kungiyar a dajin Alawa da ke yankin Shiroro a jihar.

Niger
Boko Haram ta hallaka bayin Allah Hoto: Hoto: @HQNigerianArmy/@HonBago
Asali: Twitter

Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa majiya daga yankin da kuma jami’an tsaro sun tabbatar da cewa harin ya faru ne a ranar 27 ga Fabrairu, 2027.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rahotanni sun bayyana cewa mayakan sun kai farmaki kan masu hakar ma'adinai da suka fito daga garin Bassa da wasu ƙauyuka da ke kewaye da shi.

Boko Haram ta addabi mazauna Neja

News Central TV ta wallafa cewa yankin Bassa, wanda a baya Boko Haram ta addaba da hare-hare, ya fara samun zaman lafiya bayan an tura sojoji yankin a 2024.

Sai dai tun bayan wani artabu da ya faru a watan Oktoba, inda Boko Haram ta yi asarar dakarunta, kungiyar ta ƙara tsananta kai hare-haren sari-ka-noke.

Yan ta'adda
Ana zargin Boko Haram ta kai harin ramuwar gayya Hoto: @ZagazOlaMakama
Asali: Twitter

Sun fara dasa abubuwan fashewa da kai hare-hare a ƙauyukan da ba su da isasshen kariya daga jami’an tsaro.

Kara karanta wannan

Ana neman Turji, wani ɗan bindiga da yaransa sun ba da mamaki, sun mika wuya

Tsofaffin 'yan ƙungiyar sun tabbatar da cewa a artabun watan Oktoba, an kashe mutum biyar daga ɓangaren Boko Haram, har da wani kwararren masanin fashewa mai suna Baba Adamu.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa harin da aka kai a ranar 27 ga Fabrairu na iya zama ramuwar gayya kan asarar da kungiyar ta yi.

Boko Haram ta farmaki ma’aikata

Maharan sun kai farmaki ne da tsakar dare, inda suka kashe duk manyan maza da suka samu a wurin, tare da barin mata da ƙananan yara masu shekaru 10 zuwa 12.

Rahotanni sun tabbatar da cewa maharan sun kashe wasu mafarauta biyu da ke barci a wurin, wanda ya kawo yawan mutanen da aka kashe zuwa 11.

Wani mazaunin Bassa mai suna Ibrahim Tanko ya tabbatar da kisan, tare da bayyana cewa an kai wasu biyu asibitin Minna domin ceto rayuwarsu.

Zuwa yanzu, an tabbatar da binne mutum bakwai a wurin da aka kai harin, yayin da aka binne sauran mutanen a garin Bassa.

Kara karanta wannan

Ana shirin fara azumin Ramadan, mutane sama da 15 sun mutu a jihar Katsina

'Yan Boko Haram sun kai hari a Borno

A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu ‘yan ta’adda da ake zargin ‘yan kungiyar Boko Haram ne sun sace Farfesa Abubakar Eljuma, babban malami a Jami’ar Sojojin Najeriya da ke Borno.

Rahotanni sun bayyana cewa an sace Farfesa Eljuma ne a ranar Lahadi, 2 ga watan Maris, 2025, a kan titin Damaturu-Biu, kusa da garin Kamuya, wanda da ke fama da matsalar tsaro.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.

iiq_pixel