Mutuwa Mai Yankan Kauna: Fitaccen Basarake Ya Rasu, Tinubu Ya Jajantawa Al'umma

Mutuwa Mai Yankan Kauna: Fitaccen Basarake Ya Rasu, Tinubu Ya Jajantawa Al'umma

  • Shugaba Bola Tinubu ya jajantawa mutanen Remo da Gwamnatin Ogun bisa rasuwar Oba Idowu Basibo, wanda ya shafe shekaru 22 yana mulkin Iperu
  • Tinubu ya yaba wa Oba Basibo kan jagoranci na adalci da hakuri, yana mai cewa girmansa da hikimarsa za su kasance abin tunawa da ba za a manta da su ba
  • Shugaban ya yi addu’a ga marigayin, yana fatan za a ci gaba da girmama bayansa, tare da dorawa kan kyawawan ayyukansa na al’umma
  • Wannan na zuwa zuwa ne bayan tsohon sanata a jihar Ogun ya yi bankwana da duniya inda Gwamna Dapo Abiodun ya jajanta

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

FCT, Abuja - Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya miƙa ta’aziyyarsa ga al’ummar Remo da Gwamnatin Ogun bisa rasuwar fitaccen basarake a jihar.

Kara karanta wannan

Tinubu ya ba da mamaki da ya tono wani sirri tsakaninsa da IBB a 1993

Tinubu ya tura sakon ta'azziya bayan Oba Adeleke Adelekan Idowu Basibo, Sarkin Iperu da ya shekaru kan mulki ya riga mu gidan gaskiya.

Tinubu ya tura sakon ta'azziya da basarake ya kwanta dama
Bola Tinubu ya kadu bayan sanar mutuwar basarake a jihar Ogun. Hoto: Bayo Onanuga.
Asali: Facebook

Tinubu ya jajanta bayan rasuwar basarake a Ogun

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Bayo Onanuga, Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan Bayani ya fitar da Tribune ta samu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cikin sanarwar, Tinubu ya ce:

"Oba Idowu Basibo ya shafe shekaru 22 yana zaman lafiya da kawo ci gaba a Akesan-Odoru."

Sanarwar ta ce Tinubu yana girmama Oba Basibo a matsayin uba na ƙwarai ga da dama, ciki har da Gwamna Dapo Abiodun, wanda ya fito daga yankin.

Tinubu ya yaba da marigayin a matsayin shugaba na gari da ya dage kan mulki, yana mai cewa al’ummarsa sun amfana da jagorancinsa.

Tinubu ya yi ta'aziyyar mutuwar basarake a Ogun

Tinubu ya fadi alherin da marigayin ya yi

Shugaban ya tuna da martabar Oba Basibo da wayonsa, yana mai cewa shawarwarinsa za su ci gaba da zama abin tunawa a zukatan shugabanni.

Kara karanta wannan

Tazarce: Minista ya fadi jihar Arewa da Tinubu zai samu ruwan kuri'u a zaben 2027

Yayin da sarkin ke shirin gamuwa da Ubangijinsa,Tinubu ya nuna kwarin gwiwa cewa abin da ya bari zai ci gaba da ba da tasiri, cewar Leadership.

Tinubu ya kuma yi addu’a ga marigayin, yana fatan Allah ya jikansa da rahama, ya ba shi hutu har abada da kuma ba iyalansa hakurin jure wannan rashi.

'Ba za a manta da shawarwarin basaraken ba' - Tinubu

“Shawarar da ya ba shugabanni da ba su da iyaka cikin gaskiya da daraja za a tuna da su tare da girmamawa.”

- Cewar Bola Tinubu

Tsohon sanata ya yi bankwana da duniya

Mun ba ku labarin cewa mutane sun shiga alhini bayan tsohon sanatan Ogun ta Yamma, Ayodeji Otegbola ya riga mu gidan gaskiya yana da shekaru 91 a duniya.

Gwamna Dapo Abiodun na jihar Ogun ya miƙa sakon ta'aziyya ga iyalai, ƴan uwa da abokan arzikin mamacin tare da addu'ar Allah ya ba su haƙurin jure wannan rashi da suka yi.

Abiodun ya bayyana cewa mutuwar sanatan babban rashi ne ga jihar Ogun da ma Najeriya baki ɗaya, ya yi addu'ar Allah ya gafarta masa ya kuma yi masa rahama.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.