Adamawa: An Shiga Fargaba da Bindiga Ta Tashi a Wurin Ibada, Mutane Sun Jikkata

Adamawa: An Shiga Fargaba da Bindiga Ta Tashi a Wurin Ibada, Mutane Sun Jikkata

  • Wani mafarauci ya harba bindiga ba da gangan ba yayin taron cocin LCCN a Demsa da ke jihar Adamawa a Arewacin Najeriya
  • Lamarin da ya faru ya yi sanadin raunata akalla mutane takwas yayin da aka kai su asibiti suna karbar kulawa domin tabbatar da ba su kulawa
  • ‘Yan sanda sun kama mafaraucin yayin da Kwamishinan ‘yan sanda ya gargadi masu tsaron irin haka kan daukar bindiga wurin taruka
  • An bukaci mazauna Demsa su taimaka wa ‘yan sanda don gujewa irin wannan hatsari a nan gaba, domin tabbatar da zaman lafiya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Demsa, Adamawa - A kalla mutane takwas ne suka jikkata bayan da bindigar wani mafarauci ta tashi bisa kuskure.

Lamarin ya faru ne yayin yayin babban taron cocin LCCN a karamar hukumar Demsa da ke Adamawa da ke Arewacin Najeriya.

Kara karanta wannan

Matashi ya gayyaci abokinsa gida ya masa kisan wulakanci da adda, ya sassara shi

Wasu mutane 8 sun jikkata da bindiga ta tashi bisa kuskure
Mutane 8 sun samu raunuka da bindigar mafarauci ta tashi bisa kuskure a Adamawa. Hoto: Legit.
Asali: Original

Bindigar ta yi sanadin raunata mutane 8

Mafaraucin dan kungiyar masu farauta ne daga Kukta a Song, yana dauke da bindigar toka domin tsaro a wurin taron, cewar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kakakin ‘yan sanda, SP Suleiman Yahaya Nguroje, ya ce bindigar ta subuce daga hannunsa, ta tashi sau da dama, lamarin da ya jikkata mutane.

Ya kara da cewa wadanda suka jikkata suna samun kulawa a asibiti da ke Demsa, kuma ana ci gaba da bincike kan lamarin domin kare faruwar hakan a gaba.

Yan sanda sun kama faraucin a Adamawa

Nguroje ya ce an kama mafaraucin amma ba za a bayyana sunansa ba har sai an kammala bincike kan abin da ya faru a wurin taron, cewar Daily Post.

Kwamishinan ‘yan sanda, Dankombo Morris, ya yi Allah-wadai da lamarin, yana mai gargadin masu tsaron gari kan amfani da bindiga a taruka.

Ya bukaci mazauna Demsa da su hada kai da ‘yan sanda domin gujewa irin wannan hatsari a nan gaba da kuma tabbatar da zaman lafiya.

Kara karanta wannan

Magana ta girma: Trump zai binciki zargin tallafawa Boko Haram daga Amurka

Yan bindiga sun kai hari a asibitin Adamawa

Kun ji cewa Rundunar 'yan sandan Adamawa ta tabbatar da cewa wasu masu garkuwa da mutane sun sace akalla mutane hudu a jihar.

Jami'in hulda da jama'a na rundunar, SP Suleiman Nguroje ya tabbatar da kai harin da aka kai asibitin koyarwa na Maodibbo.

Lamarin ya faru ne a kauyen Mayo Kila, wani yanki da ke kusa da iyakar Najeriya da Kamaru a karamar hukumar Jada ta Jihar Adamawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.