"Tinubu Mutumin Kirki ne, Yana da Niyya Mai Kyau," Babban Malami Ya Yi wa Mutane Nasiha

"Tinubu Mutumin Kirki ne, Yana da Niyya Mai Kyau," Babban Malami Ya Yi wa Mutane Nasiha

  • Wani babban limamin coci a jihar Legas, Fasto Sam Olu Alo ya ce shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu na da kyakkyawar niyya
  • Malamin ya bukaci shugabannin addinai da ƴan Najeriya su daina zagin shugaban ƙasa, maimakon haka su dage da nema masa shiriya wurin Allah
  • Faston ya kuma shawarci gwamnati ta ƙarfafa matasa su rungumi harkar noma, yana mai cewa ita ce hanyar bunƙasa tattalin arziki

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Fitaccen malamin addini, Fasto Sam Olu Alo, ya bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da rokon Allah ya ba gwamnatin Shugaban ƙasa, Bola Tinubu nasara.

Babban limamin cocin ya jaddada cewa jagoranci na bukatar shiriya daga Allah, musamman a shekarar 2025.

Bola Tinubu.
Malamin addini ya shawarci ƴan Najeriya su rika yi wa shugabanni addu'a maimakon zaginsu Hoto: @OfficialABAT
Asali: Facebook

Ya faɗi haka ne yayin da yake jawabi a wani taro da aka shirya a cocin Jesus City da ke kan titin Lekki-Epe a jihar Legas, kamar yadda Tribune Nigeria ta kawo.

Kara karanta wannan

"Allah ne ya jaraba mu," Gwamna ya faɗawa babban malami abin da bai sani ba

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaba Tinubu na bukatar goyon baya

Fasto Alo, wanda shi ne ya kafa cocin Christ Apostolic Church (CAC), ya bukaci ‘yan kasa su mara wa shugabanninsu baya ta hanyar addu’a, don neman hikima da basira daga Allah.

Limamin cocin ya ce:

“‘Ya kamata ƴan Najeriya su ci gaba da goyon bayan Shugaba Bola Tinubu tare yi masa addu’a. Shugaban kasa yana da kyakkyawar niyya; ba ya jin dadin halin kunci da ake ciki a kasar nan."
“Duk da halin da ake ciki, idan wadanda muka zaba sun fahimci dalilin da ya sa muka ba su amanarmu, akwai bukatar mu kuma mu ci gaba da yi musu addu’a.
"Ba kowa ne ya amince da manufofin Awolowo ba, da ace duk ‘yan kasa sun goyi bayansa, da ya zama shugaban ƙasa. Amma bayan mutuwarsa mutane sun gane darajarsa.”

Mutane su nema wa shugabanni shiriya

Fasto Alo ya jaddada muhimmancin yin addu’a domin nasarar Shugaba Tinubu, yana mai cewa hakan zai sa Allah ya shiga lamarinsa kuma ya taimaka masa.

Kara karanta wannan

"Za mu kawo karshen mulkin kama karya," PDP ta musanta baraka a cikinta

“Shugabanni da aka zaba su fahimci cewa matsayin da suke kai ba hakkinsu ba ne, dama ce da suka samu. Akwai mutane da yawa da suka fi su cancanta amma ba su samu wannan dama ba.”

Malami ya bukaci a daina zagin Tinubu

Ya kuma bukaci malaman addini a faɗin Najeriya su yi wa gwamnati addu’a maimakon zagin shugabanni.

“Dole ne mu daina zagin shugabanni, mu rika ba su shawara. Ya kamata mu rika fadin abubuwa masu kyau game da kasarmu kamar yadda ‘yan kasashen da suka ci gaba ke yi.”

Sam Olu Alo ya kuma bukaci gwamnati ta karfafa wa matasa gwiwa su koma harkar noma, yana mai cewa noma na da matukar muhimmanci wajen bunkasa tattalin arzikin kasa.

Tinubu ba zai kai labari ba a 2027

A wani rahoton, kun ji cewa malamin addinin Musulunci, Sheikh Murtala Asada zai wahala shugaban kasa, Bola Tinubu ya yi tazarce a 2027.

Malamin ya bayyaɓa cewa yadda shugaban ya illata Arewacin Najeriya kaɗai zai zama sanadin faɗuwarsa a zaɓe mai zuwa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262