Mutumin da Tinubu Ya Naɗa a Muƙami Ya Tsallake Rijiya da Baya, An Yi Yunƙurin Kashe Shi
- Wasu miyagu sun farmaki babban daraktan ayyukan gine-gine na hukumar gidaje ta kasa watau FHA, Remi Omowaiye a jihar Osun
- Omowaiye, wanda tsohon kwamishina ne ya faɗa tarkon maharan a lokacin da yake hanyar zuwa Osogbo yau Litinin, 17 ga watan Fabrairu, 2025
- Ya ce miyagun sun buɗe wa motar da yake ciki wuta har sun fasa gilashin taga amma duk da haka ya samu ya tsira da ransa
CHECK OUT: Education is Your Right! Don’t Let Social Norms Hold You Back. Learn Online with LEGIT. Enroll Now!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Osun - Babban Daraktan Ayyukan Gine-gine na Hukumar Gidaje ta Tarayya (FHA), Remi Omowaiye, ya tsallake rijiya da baya a wani mummunan hari a jihar Osun.
Rahotanni sun nuna cewa mutumin wanda ke riƙe da muƙamin siyasa ya sha da kyar a harin, wanda wasu miyagu suka kai masa a kan titin Osogbo/Ilesa a ranar Litinin.

Asali: Facebook
Bisa bayanan da jaridar The Nation ta tattara, lamarin ya faru ne da misalin karfe 2:05 na rana a gaban sakatariyar ƙaramar hukumar Ilesa ta Yamma.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Mahara sun buɗe wa mutumin wuta
Maharan sun buɗe wa Mista Omowaiye, tsohon kwamishinan ayyuka a Osun wuta a lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa Osogbo.
Majiyoyi sun bayyana cewa Omowaiye ya jagoranci wasu ƴan jam’iyyar APC zuwa hedikwatar ‘yan sanda a Ilesa domin neman kariya ga shugabannin kananan hukumomi da aka mayar.
Bayan sun bar ofishin ƴan sanda sun koma hedikwatar APC, kuma daga nan aka sallame kowa ya koma gida.
Yadda hadimin gwamnatin Tinubu ya tsira
Sai dai yayin da Omowaiye ya kama hanyar komawa Osogbo a cikin wata Toyota Hummer mai launin fari, maharan suka yi masa kwanton ɓauna.
An ce ya faɗa tarkon tsagerun ne a gaban sakateriyar ƙaramar hukumar Ilesa ta Yamma, inda aka farfasa motarsa da ruwan alburusai.
A wata hira da yayi da Punch bayan harin, Omowaiye ya bayyana cewa direbansa da wani ɗan sanda sun samu munanan raunuka.
Diraba da ɗan sanda sun samu raunuka
"Ina kan hanyar dawowa daga Ilesa zuwa Osogbo lokacin da muka ci karo da miyagun sun mana kwanton ɓauna. Sun buɗe wa inda nake zaune wuta, har alburusai suka fasa taga."
"Direbana da ɗan sandan da ke tare da mu sun sami munanan raunuka. An garzaya da su asibiti domin samun kulawa."
Har ila yau, Omowaiye ya bayyana cewa an kai wa motar sabon shugaban Ilesa ta Gabas hari a daidai wajen da aka yi masa kwanton ɓauna.
Ya yi kira ga hukumomi da su binciki lamarin tare da tabbatar da an hukunta waɗanda suka aikata wannan aika-aika.
An kashe ciyaman da wasu a Osun
Kuna da labarin cewa shugaban ƙaramar hukumar Irewale ya rasa ransa tare da wasu da dama da ciyamomin suka yi yunƙurin komWa ofis.
Hon. Abass ya jagoranci wasu shugabannin kananan hukumomi da aka sallama don karbe ofishin karamar hukumar bisa ga hukuncin kotu.
Asali: Legit.ng