Gwamnan Bauchi Ya Kasa Hakura, Ya Yi Wa Ministan Tinubu Martani Mai Zafi

Gwamnan Bauchi Ya Kasa Hakura, Ya Yi Wa Ministan Tinubu Martani Mai Zafi

  • Gwamnatin jihar Bauchi ba ta ji daɗin sukar da ministan harkokin ƙasashen wajje, Yusuf Tuggar, ya yi wa Gwamna Bala Mohammed ba
  • Shugaban ma'aikatan fadar gwamnatin jihar Bauchi ya zargi ministan da gazawa a muƙamin da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ba shi
  • Aminu Hassan Gamawa ya bayyana cewa ministan bai san abubuwan da ke faruwa ba a jihar saboda yawace-yawacen da yake yi a ƙasashen waje

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Bauchi - Gwamnatin jihar Bauchi ta yi martani mai zafi ga ministan harkokin ƙasashen waje a gwamnatin Bola Tinubu, Yusuf Tuggar.

Martanin na zuwa ne bayan ministan ya caccaki gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed kan sukar da yake yi wa ƙudirin haraji.

Gwamnan Bauchi ya caccaki ministan Tinubu
Gwamnanatin Bauchi ta caccaki Yusuf Tuggar Hoto: @SenBalaMohammed, @NigeriaMFA
Asali: Twitter

Martanin na cikin wata sanarwa ne da shugaban ma'aikatan fadar gwamnatin Bauchi, Aminu Hassan Gamawa, ya fitar a madadin gwamnan, cewar rahoton jaridar Daily Trust.

Kara karanta wannan

Yaki da talauci: Gwamnan Jigawa ya raba tallafin kudi ta katin ATM

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamnatin Bauchi ta caccaki Yusuf Tuggar

Dr. Aminu Hassan Gamawa ya bayyana Yusuf Tuggar a matsayin mara ƙwarewa a diflomasiyya mai neman damar siyasa don moriyar kansa, rahoton jaridar The Punch ya tabbatar.

Gamawa ya zargi Yusuf Tuggar da rashin kallon gazawarsa a muƙamin da aka ba shi, amma ya maida hankali wajen sukar gwamnan Bauchi.

Shugaban ma'aikatan fadar gwamnatin ya bayyana cewa ministan ya gaza a aikinsa amma ya fi mayar da hankali kan sukar Gwamnan Bauchi, wanda manufofinsa a ɓangaren noma suka jawo tagomashi ga jihar Bauchi.

"Abin mamaki ne cewa Tuggar, wanda ɗan asalin Bauchi ne, bai san waɗannan abubuwan ba. Idan da yana zama a jiharsa maimakon yawan yawace-yawace a ƙasashen waje, da ya fahimci irin sauyin da Bala Mohammed ya kawowa Bauchi."
"Rashin kusancinsa da talakawa da kuma yankinsa, wanda har shugaba Bola Tinubu bai iya cin zaɓe a can ba, yana nuna rashin tasirinsa a wurin mutanen da yake iƙirarin wakilta."

Kara karanta wannan

"Ba kamar Tinubu ba": Amaechi ya fadi yadda ya shirya samar da sauki ga talaka

Ministan Tinubu ya jawowa Najeriya abin kunya

Har ila yau, shugaban ma'aikatan fadar gwamnatin ya zargi Tuggar da gazawa wajen jagorantar ECOWAS, wacce a baya ƙungiya ce mai ƙarfi da haɗin kai, amma yanzu tana fuskantar rikice-rikice.

"Gurguwar shawararsa ga shugaba Tinubu kan rikice-rikicen yankin Sahel ya haifar da ficewar ƙasashe masu muhimmanci kamar Mali, Burkina Faso, da Nijar daga ƙungiyar."
"Wannan gagarumar gazawa ce da ba a taɓa yin irinta ba a tarihin jagorancin Najeriya a yankin Afirika ta Yamma."

Shugaban ma’aikatan fadar gwamnaatin ya bayyana cewa zargin da Tuggar ya yi wa Bala Mohammed dangane da amfani da filaye a Bauchi ƙarya ce kawai don ɓata suna.

Dogara ya faɗi yadda aka taimaki gwamnan Bauchi

A wani labarin kuma, kun ji cewa tsohon shugaban majalisar wakilai, Yakubu Dogara, ya bayyana aka taimaki gwamnan Bauchi, ya samu tikitin takarar PDP a zaɓen 2019.

Yakubu Dogara ya bayyana cewa ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya yi wa Bala Mohammed riga da wanda a lokacin amma yanzu ya koma yana yi masa butulci.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng

iiq_pixel