Shugaba Tinubu Ya Kara Gwangwaje Gawuna da Muƙami, Ya ba Shi Kujera Mai Girma

Shugaba Tinubu Ya Kara Gwangwaje Gawuna da Muƙami, Ya ba Shi Kujera Mai Girma

  • Tsohon mataimakin gwamnan Kano kuma ɗan takarar jam'iyyar APC a zaɓe 2023, Dr. Nasiru Gawuna ya sake samun mukami a gwamnatin tarayya
  • Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Nasiru Gawuna a matsayin shugaban majalisar gudanarwa na bankin Mortgage na ƙasa
  • Wannan dai na zuwa ne bayan naɗin da shugaban ƙasar ya yi ws Gawuna a 2024, inda aka ba shi muƙamin shugaban gudanarwa na Jami'ar BUK ta Kano

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja - Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya sake naɗa ɗan takarar gwamnan jihar Kano a inuwar APC a zaɓen 2023, Dr. Nasiru Gawuna a muƙami a gwamnatin tarayya.

Mai girma shugaban kasa ya naɗa Gawuna a matsayin shugaban majalisar gudanarwa na bankin Mortgage, mai ba da lamunin gidaje a Najeriya.

Nasir Gawuna da Bola Tinubu
Bola Tinubu ya ƙara naɗa tsohon mataimakin gwamnan Kano, Nasiru Gawuna a muƙami Hoto: Bola Ahmed Tinubu, Nasiru Gawuna
Asali: Facebook

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya wallafa a shafin X yau Juma'a.

Kara karanta wannan

'Dan Majalisar Tarayya na Kano na tsaka mai wuya, yunƙurin tsige shi ya kara tsananta

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaba Tinubu ya ba Gawuna muƙami

Kafin wannan naɗin, Gawuna, tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano shi ne shugaban majalisar gudanarwa ta Jami'ar Bayero watau BUK.

Shugaba Bola Tinubu ya naɗa Gawuna a wannan muƙami a Jami'ar BuK ne a shekarar 2024.

Nasiru Yusuf Gawuna ya zama mataimakin tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje bayan murabus din Farfesa Hafiz Abubakar a karshen shekarar 2018.

Bayan kammala wa'adi biyu na Ganduje. ya tsayar da Gawuna a matsayin wanda zai gaje shi a inuwar APC amma ya sha ƙasa a hannun NNPP.

Yadda Gawuna ya nemi zama gwamnan Kano

Guguwar jam'iyyar NNPP karkashin jagoranci tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso ce ta hana Nasiru Gawuna zama magajim Ganduje.

Gwamna Abba Kabir Yusuf wanda ya fi shahara da Abba Gida-Gida a lokacin zaɓe, shi Allah ya ɗora a kujera lamba ɗaya a Kano a zaɓen 2023.

Hakan ya sa a 2024, shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Nasiru Gawuna a matsayin shugaban majalisar gudanarwa a Jami'ar BUK.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya shiga yanayi da yayan gwamna ya riga mu gidan gaskiya

Kusan shekara guda bayan wannan naɗi, yanzu kuma Bola Tinubu ya saƙe naɗa shi a matsayin shugaban majalisar gudanarwa na bankin ba da lamuni watau Mortgage Bank.

Gawuna da Ganduje sun samu sababbin muƙamai

Shugabar ƙasar ya sanar da naɗin Gawuna ne tare da wasu mutum 44 da aka naɗa a hukumomin gwamnati daban-daban.

Daga cikin waɗanda suka samu muƙami a sababbin naɗe-naɗen Tinubu har da mai gidan Gawuna kuma shugaban APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje.

Mai girma shugaba Tinubu ya naɗa Ganduje a matsayin shugaban Majalisar gudanarwa na hukumar kula da harkokin jiragen sama watau FAAN.

Tinubu ya amince a rabawa talakawa N4bn

A wani labarin, kun ji cewa Shugaba Tinubu ya amince a rabawa ƴan Najeriya masu ƙaramin karfi Naira biliyan 4.

Ana fatan shirin rabon tallafin zai amfani gidaje miliyan 10 da suka fi fama da matsaloli, musamman waɗanda suka rasa matsugunansu a Arewa maso Gabas

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262