Gwamna Bala Mohammed Ya Sauya Sakataren Gwamnati, An Nada Sabon SSG

Gwamna Bala Mohammed Ya Sauya Sakataren Gwamnati, An Nada Sabon SSG

  • Gwamnan Bauchi, Bala Mohammed ya nada sabon Sakataren gwamnati tare babban sakatarensa bisa wasu dalilai
  • Tsohon Sakataren gwamnatin jihar, Barista Kashim Ibrahim ya ajiye aiki ba tare da an bayyana dalilan hakan ba
  • A wannan rana ne za a ranstar da sabbabin wadanda aka nada mukaman biyu, inda aka bayya gogewarsu a kan aiki

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Bauchi - Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya maye gurbin Barista Kashim Ibrahim da Aminu Hammayo a matsayin Sakataren Gwamnatin Jiha (SSG).

Haka kuma, ya maye gurbin tsohon Babban Sakatare ga gwamna, Samaila Burga, wanda ya yi murabus domin zama Shugaban Jam’iyyar PDP a jihar.

Bauchi
Gwamnan Bauchi ya yi sabbin nade-nade Hoto: Sen. Bala Mohammed
Source: Facebook

The Guardian ta ce a sanarwar da Mukhtar Gidado, mai magana da yawun gwamnan, ranar Juma’a an ce Hashimu Kumbala ne ya maye gurbin Burga, yayin da Hammayo ya zama sabon SSG.

Kara karanta wannan

"Wannan lokaci ne na hakuri," Gwamnan Legas ya mika ta'aziyya ga gwamna Namadi

Dalilin sauya SSG a jihar Bauchi

Jaridar Blueprint ta ruwaito cewa Barista Kashim Ibrahim ya yi murabus daga mukamin Sakataren Gwamnatin Jiha ba tare da an bayyana dalilin ba.

Mukhtar Gidado ya bayyana cewa;

"Hammayo gogaggen ma’aikaci ne wanda ya yi fice wajen gudanar da ayyukansa a matsayin jami’in gwamnati, ya yi suna wajen kwarewa, aiki tukuru, da sadaukarwa wajen hidimar al’umma."

Za a rantsar da masu mukaman Bauchi

Aminu Hammayo, wanda ya taba zama SSG a baya, kafin wannan sabon nadin nasa, shi ne kwamishinan tsare-tsare da kasafin kudi na jihar Bauchi.

Gwamnati ta bayyana cewa:

“A matsayinsa na SSG, zai bayar da mahimmin goyon baya na gudanarwa da shawara ga gwamna, tare da tabbatar da daidaito a tsakanin hukumomin gwamnati."

Dukkannin sababbin masu mukaman, Aminu Hammayo da Hashimu Kumbala za su sha rantsuwar fara aiki a yau.

Gwamnan Bauchi ya aika sako ga Tinubu

A baya kun ji cewa gwamnan Bauchi, Bala Mohammed ya tunatar da gwamnatin Najeriya, karkashin mulkin Bola Ahmed Tinubu irin wahalar da jama'a ke ciki na kunci.

Kara karanta wannan

Ministan Tinubu ya tona yadda ya samawa 'yan jiharsa ayyukan tarayya masu yawa

Sai dai ya shaida wa mazauna jihar Bauchi cewa ya na aiki tukuru da taimakon mukarrabansa wajen kawo sauki ga halin da ake ciki na matsi da kuncin rayuwa da ake ji.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng