Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi ga 'Yan Najeriya, Ya Sanya Lokacin Hirar Farko
- Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai tattauna da ƴan jarida a karon farko tun bayan hawansa kan madafun ikon ƙasar nan
- Mai taimakawa shugaban ƙasa kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa za a yi tattaunawar ne a daren ranar Litinin
- Onanuga ya ƙara da cewa za a watsa tattaunawar ne a tashar talabijin ta NTA da gidan rediyon FRCN da misalin ƙarfe 9:00 na dare
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
Jihar Legas - Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai tattauna da ƴan jarida a karon farko.
Shugaba Tinubu zai yi tattaunawar ne wacce ita ce ta farko tun bayan hawansa mulki a ranar Litinin, 23 ga watan Disamban 2024.

Asali: Twitter
Tinubu zai yi hirar farko da ƴan jarida
Mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a shafinsa na X.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Za a watsa tattaunawar ne a gidan talabijin na Najeriya (NTA) da kuma gidan rediyon tarayyar Najeriya (FRCN).
Bayo Onanuga ya ce za a watsa tattaunawar ne da misalin ƙarfe 9:00 na daren yau Litinin.
"Za a watsa tattaunawar farko da ƴan jarida tare da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, da ƙarfe 9:00 na dare a ranar Litinin, 23 ga watan Disamba, a tashar NTA da gidan rediyon FRCN."
"Ana buƙatar tashoshin talabijin da gidajen rediyo su kama domin tattaunawar."
- Bayo Onanuga
Karanta wasu labaran kan Bola Tinubu
- "Ba abin da za a fasa," Bola Tinubu ya sake magana mai ɗumi kan kudirin haraji
- Gwamnatin Tinubu ta karbo bashin Naira tiriliyan N5.84, an fadi ayyukan da aka yi
- Kasafin kudi: Yadda gyara gidajen Tinubu, Shettima za su lakume N6.36bn
Gwamnati sun raba tiriliyoyi a Najeriya
A baya rahoto ya zo cewa Naira tiriliyan 3.14 ya shigo cikin asusun gwamnatin tarayya kuma an raba Naira tiriliyan 1.7 daga asusun FAAC a watan Nuwamban 2p24.
Gwamnatin tarayya ta samu N580bn, an raba N549bn tsakanin gwamnonin jihohi 36 sannan shugabannin kananan hukumomin sun samu N402.55bn.
Asali: Legit.ng