'Akwai Aiki a gabanku': Aminu Ado Bayero Ya Shawarci Malamai da Limamai kan 'Yan Daba

'Akwai Aiki a gabanku': Aminu Ado Bayero Ya Shawarci Malamai da Limamai kan 'Yan Daba

  • Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero ya nuna damuwa kan yadda yan daba suka addabi al'umma a Kano
  • Basaraken ya bukaci iyayen yara da hukumomi da su kara sanya ido wurin tabbatar da kula da 'ya'yansu
  • Hakan ya biyo bayan yawan ayyukan ta'addanci da ya zama ruwan dare wanda ya yi ajalin rayuka a jihar Kano

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero ya koka kan ayyukan yan daba a jihar musamman a 'yan kwanakin nan.

Basaraken ya yi kira ga al'ummar jihar da su zauna lafiya da juna domin samun cigaba a Kano da ta yi fice a wajen kasuwanci.

Aminu Ado Bayero ya gargadi iyaye da hukumomi kan ayyukan yan daba
Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero ya koka kan ayyukan yan daba. Hoto: Masarautar Kano.
Asali: Facebook

Aminu Ado ya koka kan ayyukan daba a Kano

Aminu Ado Bayero ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da Masarautar Kano ta wallafa a shafin Facebook.

Kara karanta wannan

Karanci kudi: CBN ya gano masu jawo matsalar, ya fadi tarar da zai ci bankuna

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya kuma bukaci al'umma su cigaba da kaunar juna a tsakaninsu tare da gujewa duk wani abu da zai kai ga tayar da zaune tsaye ko fadan daba.

Mai martaban ya koka kan yadda yan jihar suka tsinci kansu, musamman a rikice-rikicen daba da suka jawo asarar rayuka a cikin birnin Kano.

"Ina kira ga limaman masallacin Juma'a da malamai da su cigaba da wa'azi da kuma fadakar da al'umma."
"Ina tunatar da hukumomi da jagororin al'umma da su kula da nauyin da Allah ya daura musu na kare da lafiya da dukiyoyi."

- Cewar sanarwar

Yan daba: Aminu Ado ya shawarci iyayen yara

A kan haka, Sarkin ya bukaci iyaye su kasance masu lura da amanar ‘ya’yan da Allah ya ba su kan nauyin da ya dora musu.

Haka zalika, Sarkin na 15 ya tunatar da gwamnatocin jihohi da jagororin al’umma su kula da nauyin da ke kansu na tabbatar da lafiya da kariya ga rayuka da dukiyoyi.

Kara karanta wannan

'Na fasa': Gwamna ya turje kan sabon albashin N80,000, ya fadi sharuda ga NLC

Kotu ta dakatar da Aminu Ado daga gyaran masarauta

Kun yi cewa wata babbar kotun Kano ta yi hukunci kan buƙatar gwamnatin jihar ta hana Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero gyara fadar Nasarawa.

Kotun ƙarƙashin jagorancin Mai shari'a Dije Abdu-Aboki ta sake hana shi gyara fadar Nasarawa da yake zaune a cikinta bayan an sauke shi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

iiq_pixel