Kwana 70 Babu Wutar Lantarki: 'Yan Kasuwar Kano Sun Yi Gangamin Sallar Alƙunuti
- Masu kanana da matsakaitan masana’antu a Dakata, karamar hukumar Nassarawa a jihar Kano sun gudanar da sallar Alkuniti
- 'Yan kasuwar sun ce sun shirya addu'ar ne bayan shafe tsawon kwanaki 70 ba tare da samun wutar lantarki daga KEDCO ba
- A cewarsu, sama da 'yan kasuwa 10,000 ne rashin wutar lantarkin ya shafa kuma hakan ya janyo masu asarar miliyoyin Naira
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Kano - Al'ummar da ke zaune a Dakata, karamar hukumar Nassarawa a jihar Kano sun shafe kwanaki 70 kenan ba tare da wutar lantarki ba.
Rahoto ya nuna cewa kamfanin da ke samar da wuta a Kano da kewaye (KEDCO) bai kai wuta yankin Dakata ba na tsawon wadannan kwanaki.

Asali: Twitter
Mutanen Kano sun yi kunutin rashin wuta
Sakamakon rashin wutar, 'yan kasuwar Dakata sun yi gangamin addu'o'i tare da yin Alkunuiti kan duk wanda ke da hannu a lamarin, a cewar rahoton Daily Trust.

Kara karanta wannan
Siyasar Kano: Barau ya bukaci majalisa ta mayar da sunan Yusuf Maitama a jami'ar FUE
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A cewar 'yan kasuwar, sama da masu kananun sana'a 10,000 (SMEs) ne rashin wutar lantarkin ya jawo masu asarar miliyoyin Naira a yakin Dakata.
Sun yi Sallar Nafila tare da yi addu’ar Allah ya hukunta duk wadanda ke da hannu a halin da suke ciki.
'Yan soshiyal midiya sun yi tsokaci
@Yinkalayioye:
"Tikitin Muslim-Muslim na aiki, kuma muna son hakan."
@Corperemma_001
"Sau tari sai dai mu koma yin addu'a idan muka zabi shugabannin da ba su dace ba."
@habibb2k
"Wannan na da cikin kuskuren zabar shugabanni saboda addini, kabilanci ko son zuciya."
@AishaTafida5
"Ba ma su ga komai ba ma damar ire iren wadannan shugabannin ne za su ci gaba da zaba."
Abba zai kashe N1.7bn a gyaran wuta
A wani labarin, mun ruwaito cewa majalisar zartarwar jihar Kano karkashin shugabancin Gwamna Abba Kabir Yusuf za ta kashe N1.7bn a gyaran wutar lantarki.
Gwamna Abba ya ce za a yi amfani da kudin wajen sayo sababbin na'urorin rarraba wutar lantarki guda 500 da za a rabasu a dukkanin kananan hukumomin jihar.
Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.
Asali: Legit.ng