Ana Masa Dawo Dawo Karo na 2, Jonathan Ya Yi Magana kan Nasarar Trump

Ana Masa Dawo Dawo Karo na 2, Jonathan Ya Yi Magana kan Nasarar Trump

  • Tsohon shugaban kasa, Dakta Goodluck Ebele Jonathan ya taya sabon shugaban Amurka, Donald Trump murna
  • Jonathan ya ce tabbas Amurkawa sun tabbatar da amincewarsu ga Trump wanda ake sa ran zai kawo zaman lafiya a duniya
  • Wannan na zuwa ne yayin da wasu ke kiran dawo-dawo ga Jonathan musamman bayan Trump ya sake nasara a karo na biyu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Tsohon shugaban kasar Najeriya, Dakta Goodluck Jonathan ya yi magana kan zaben Amurka.

Jonathan ya taya sabon shugaban kasar, Donald Trump murna kan nasarar da ya samu a zaben da aka gudanar.

Jonathan ya taya Donald Trump murnar lashe zabe
Goodluck Jonathan ya taya sabon shugaban Amurka, Donald Trump murnar lashe zabe. Hoto: @GEJonathan.
Source: Twitter

Jonathan ya fadi tasirin nasarar Trump a duniya

Kara karanta wannan

Atiku ya fadi mutum 1 da ya yi kokarin sulhunta shi da Obasanjo lokacin mulkinsu

Tsohon shugaban kasar ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa a yau Lahadi 10 ga watan Nuwambar 2024 a shafinsa na X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jonathan ya ce wannan nasara ta Donald Trump ya nuna yadda Amurkawa suka aminta da shi da kuma tsare-tsarenda tun a baya.

Ya ce yana da tabbacin nasarar ba iya Amurkawa za ta amfana ba har ma da zaman lafiyar duniya baki daya duba da yadda ya dauko tsare-tsarensa tun farko.

Jonathan ya taya Donald Trump murnar lashe zabe

"Ina taya ka murna samun nasara da ka yi a matsayin shugaban kasar Amurka na 47 bayan kammala zabe a kwanakin nan."
"Wannan nasara taka ta nuna yadda Amurkawa suka aminta da dukan tsare-tsaren da shirya musu."
"Ina da tabbacin nasarar ba iya inganta mafarkin Amurkawa za ta yi ba, har ma da kawo zaman lafiya da cigaba a duniya."

- Goodluck Jonathan

Jonathan ya fadi halin da ya shiga a 2015

Kara karanta wannan

Jill Stein da ‘yan takaran da suka nemi mulkin Amurka tare da Trump da Harris

Kun ji cewa tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya tuno lokacin da ya fadi zaben da aka gudanar a 2015 a hannun Muhammadu Buhari.

Jonathan ya bayyana irin mummunan yanayi da ya shiga kan faduwa zaben, ya ce ba abu ba ne mai sauki a rayuwa a rasa mulki.

Tsohon shugaban kasar ya ce ba zai taba mantawa da marigayi Raymond Dokpesi ba kan yadda ya tsaya tare da shi a wancan lokaci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.