A Ƙarshe, Gwamnatin Tinubu Ta Fadi Dalilin Gaza Kama Yahaya Bello

A Ƙarshe, Gwamnatin Tinubu Ta Fadi Dalilin Gaza Kama Yahaya Bello

  • Yan Najeriya suna cigaba da sukan gwamnatin Bola Ahmed Tinubu kan gaza mika Yahaya Bello ga hukumar EFCC
  • Sai dai hadimin Bola Tinubu, Bayo Onanuga ya wanke gwamnatin tarayya kan cewa akwai dalilin da yasa ba su iya kama tsohon gwamnan ba
  • A yanzu haka hukumar EFCC na cigaba da neman Yahaya Bello kan wasu makudan kudi da aka zarge shi da karkatarwa a jihar Kogi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

FCT, Abuja - Gwamnatin tarayya ta wanke kanta kan rashi taimakawa EFCC ta kama Yahaya Bello.

Gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta bayyana cewa tana bin doka da oda ne a kan kokarin kama Yahaya Bello da EFCC ke yi.

Kara karanta wannan

Kusa a PDP ya soki Tinubu kan kyale Mawatalle a mukaminsa, ya fadi illar haka

Yahaya Bello
Gwamnatin tarayya ta fadi dalilin gaza kama Yahaya Bello. Hoto: Economic and Financial Crimes Commission|Alhaji Yahaya Bello
Asali: Twitter

Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ne ya yi bayani a wata hira da Channels Television ya wallafa a Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Dalilin gaza kama Yahaya Bello

Mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya ce Yahaya Bello na buya a cikin rigar kariyar gwamnan Kogi.

Bayo Onanuga ya ce gwamna Usman Ododo yana da rigar kariya kuma duk wanda ya fake a karkashinsa ba za a iya kama shi ba.

Onanuga ya bayyana cewa lamarin ba a kan Yahaya Bello ya fara faruwa a duniya ba. Ga abin da ya ce:

"Jami'an DSS da yan sanda ba za a su iya komai ba wajen kama Yahaya Bello idan ya buya a gidan gwamna Usman Ododo.
Gwamna Usman Ododo yana da rigar kariya, idan aka kama wanda ya fake a karkashinsa an karya doka.

Kara karanta wannan

Ana cikin halin kunci, Tinubu ya ware gwamna 1 a Najeriya, ya yaba masa

A karkashin haka, yan sanda da DSS ba za su iya taimakawa EFCC ba a kan lamarin."

-Bayo Onanuga

Hukumar EFCC na cigaba da neman Yahaya Bello ido rufe kuma ita ma ta zargi gwamnan Kogi da ba shi kariya.

Jigawa ta fita daga shari'a da EFCC

A wani rahoton, kun ji cewa gwamnatin jihar Jigawa ta sanar da ficewarta daga ƙarar da ke neman a soke hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa (EFCC).

Rahotanni na nuni da cewa kwamishinan shari'a na jihar Jigawa ne ya sanar da janyewar a ranar Asabar, 26 ga watan Oktoban 2024

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng