Jerin Kananan Ministoci da Suka Koma Manya bayan Tinubu Ya Yi Garambawul

Jerin Kananan Ministoci da Suka Koma Manya bayan Tinubu Ya Yi Garambawul

  • Shugaban kasa, Bola Tinubu ya yi sauye-sauye a mukaman Ministoci a gwamnatinsa bayan watanni ana jira
  • Tinubu ya sallami wasu Ministoci biyar daga gwamnatinsa yayin da ake kiraye-kiraye kan korar wasu daga cikinsu
  • Bayan sallamar Ministocin, Tinubu ya kuma amince da nadin sababbi domin maye gurbinsu da kuma hade wasu ma'aikatu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Shugaba Bola Tinubu ya sallami wasu Ministoci biyar inda ya amince da nadin wasu guda bakwai a yau Laraba 23 ga watan Oktoban 2024.

Fadar shugaban kasar ta ruwaito cewa shugaban ya karawa wasu ƙananan Ministoci zuwa manya a ma'aikatu daban-daban.

Jerin sababbin Ministoci da Tinubu ya nada
Kananan Ministoci da suka samu karin girma a gwamnatin Bola Tinubu. Hoto: Bayo Onanuga.
Asali: Facebook

Daily Trust ta tabbatar da cewa shugaban ya yi sauye-sauye a ma'aikatu bayan hade wasu daga cikinsu wanda ya tilasta sallamar Ministocin guda biyar.

Kara karanta wannan

A ƙarshe, Bola Tinubu ya maye gurbin Betta Edu, ya naɗa sabon ministan jin ƙai

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ministocin da aka karawa matsayi

Legit Hausa ta duba Ministocin da suka samu karin girma daga matsayinsu zuwa manyan Ministoci.

1. Morufu Alausa - Ministan Ilimi

Bola Tinubu ya daga matakin Alausa daga karamin Ministan lafiya zuwa babban Minista a ma'aikatar Ilimi.

Nadin Alausa ya biyo bayan sallamar Farfesa Tahir Mamman daga mukaminsa a yau Laraba 23 ga watan Oktoban 2024.

2. Imaan Sulaiman-ibrahim - Ministar mata

Imaan Sulaiman-ibrahim ta maye gurbin tsohuwar Ministar harkokin mata, Uju Kennedy-Ohanenye a yau Laraba.

Kafin nadin nata, Imaan wacce ta fito daga jihar Nasarawa ita ce karamar Ministar harkokin yan sanda a Najeriya.

3. Ayodele Olawande - Ministan cigaban matasa

Ayodele Olawande ya samu karin girma zuwa muƙamin babban Ministan cigaban matasa a yau Laraba 23 ga watan Oktoban 2024.

Kara karanta wannan

'Ba mu yarda ba': Wani dattijo ya nuna Tinubu da yatsa kan rusa ma'aikatar Neja Delta

Kafin wannan nadin, Olawande ya kasance karamin Minista a ma'aikatar cigaban matasa inda ya zama babban Minista.

Tinubu ya yi garambawul a gwamnatinsa

A baya, kun ji cewa shugaba Bola Tinubu ya rushe wasu ma'aikatu a Najeriya tare da yin sauye-sauye a mukaman Ministoci.

Bola Tinubu ya rushe ma'aikatar harkokin wasanni da kuma Neja Delta inda ya hade wasu ma'aikatu daban-daban a kasar.

Wannan na zuwa ne bayan korafe-korafe da yan Najeriya suka rika yi domin shugaban ya sallami wasu daga cikin Ministocinsa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.