Bola Tinubu Ya Ɗauko Ministan Buhari, Ya Naɗa Shi a Muƙami Bayan Korar Ministoci

Bola Tinubu Ya Ɗauko Ministan Buhari, Ya Naɗa Shi a Muƙami Bayan Korar Ministoci

  • Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗin Sunday Dare a matsayin mai ba da shawara kan harkokin sadarwa da wayar da kan jama'a
  • Sunday Daye dai ya yi aiki a matsayin ministan matasa da bunkasa harkokin wasanni a gwamnatin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari
  • Fadar shugaban ƙasa ce ta tabbatar da wannan naɗi a wata sanarwa ranar Laraba bayan korar ministoci biyar daga aiki

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

State House, Abuja - Shugaba Bola Tinubu ya nada Sunday Dare a matsayin mai ba shi shawara na musamman kan harkokin sadarwa da wayar da kan jama’a.

Sunday Dare, mai sarautar Agbaakin na Ogbomoso, ya yi aiki a matsayin ministan harkokin matasa da wasanni a gwamnatin Muhammadu Buhari.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya aika muhimmin saƙo ga ministoci 5 da ya kora daga aiki

Bola Tinubu da Sunday Dare.
Shugaba Tinubu ya nada Sunday Dare a matsayin hadiminsa Hoto: Sunday Dare
Asali: Twitter

Fadar shugaban ƙasa ta tabbatar da naɗin tsohon ministan a wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba, 23 ga watan Oktoba, 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mista Dare ya kasance kwararren ɗan jarida kuma ɗaya daga cikin waɗanda suka kafa jaridar mako-mako ta The News and Tempo, sannan ya yi aiki a ƙasar Amurka.

An haife shi a ranar 29 ga Mayu, 1966. Ya yi karatun digiri na farko a Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria (ABU) inda ya karanci kwas din 'B.Sc International Studies."

Sannan ya yi digiri na biyu a Jami'ar Jos da ke jihar Filato kuma ya kammala da sakamako mafi daraja a fannin ilimin sanin doka watau Law.

Karin bayani na nan tafe...

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Tags: