Shugaba Tinubu Ya Aika Muhimmin Saƙo Ga Ministoci 5 da Ya Kora Daga Aiki

Shugaba Tinubu Ya Aika Muhimmin Saƙo Ga Ministoci 5 da Ya Kora Daga Aiki

  • Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya aika sakon godiya da fatan alheri ga tsofaffin ministoci biyar da ya sallama daga aiki
  • A wata sanarwa da fadar shugaban ƙasa ta fitar, Tinubu ya gode masu bisa aikin da suka yi wa ƙasa a tsawon lokacin da suna ɗauka a bakin aiki
  • Shugaban kasar ya kuma ja hankalin sababbin ministocin da ya naɗa da cewa ya kamata su fahimci kudirin gwamnatinsa na kawo ci gaba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya godewa ministocin da ya kora daga aiki bisa gudummuwar da suka ba gwamnatinsa da ƙasa baki ɗaya.

Shugaban ƙasar ya yi masu fatan alheri a dukkan lamurran da za su sa a gaba, inda ya ce Najeriya ba za ta manta da hidimar da suka yi ba.

Kara karanta wannan

Ministoci: Tinubu ya nada matar Ojukwu da Ministan Buhari da wasu 5

Shugaba Bola Tinubu.
Bola Tinubu ya godewa tsofaffin ministocin da ya sallama daga aiki Hoto: @aonanuga1956
Asali: Twitter

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da mai taimaka shugaban kasa kan harkokin midiya, Dada Olusegun ya wallafa a shafin X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaba Tinubu ya kori ministoci 5

Idan baku manta ba Tinubu ya sallami ministoci biyar daga aiki a garambawul din da ya yi a majalisar zartaswa ta ƙasa.

Waɗanda aka sallama sun haɗa da Ministan harkokin yawon buɗe ido, Lola Ade John, Ministan ilimi, Farfesa Tahir Mamman da Ministar mata, Uju-Ken Ohanenye.

Sauran sune ƙaramin ministan gidaje da raya birane, Abdullahi Gwarzo da kuma Ministar matasa, Jamila Ibrahim.

Sakon Tinubu ga korarrun ministoci da sababbi

Sanarwar ta ce:

"Shugaban ƙasa ya godewa ministoci masu barin gado bisa aikin da suka yi wa ƙasa, sannan yana masu fatan alheri a duk abin da suka sa a gaba."

Bayan haka Shugaba Tinubu ya bukaci sabbabin ministocin da ya naɗa da waɗanda ya sauyawa wurin aiki da su shirya yiwa ƙasa hidima.

Kara karanta wannan

A karshe, Tinubu ya ji korafe korafen yan Najeriya, ya sallami Ministoci 5

Ya ƙara da cewa dole dukkan waɗanda aka naɗa su gane kokarin da gwamnati ke yi wajem ɗora Najeriya kan turbar ci gaba da mai ɗorewa.

Ku saurari ƙarin bayani...

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262