Ana Rade Radin Rigimar Abba da Kwankwaso, an Kori Yan Jaridu daga Gidan Gwamnati

Ana Rade Radin Rigimar Abba da Kwankwaso, an Kori Yan Jaridu daga Gidan Gwamnati

  • Gwamnatin Kano karkashin jagorancin Abba Kabir Yusuf ta dakatar da yan jaridu 14 daga gidan gwamnatin jihar
  • Rahotanni sun tabbatar da cewa wadanda abin ya shafa suna wakiltar gidajen jaridu ko rediyo daban-daban a cikin gidan gwamnatin
  • Mai magana da yawun Gwamna Abba Kabir a jihar, Sanusi Bature Dawakin Tofa shi ya ba da umarnin a cikin wata sanarwa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano - Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da yan jaridu 14 daga daukar rahoto a gidan gwamnati.

Gwamantin jihar da umarci dukan wadanda abin ya shafa da su koma wuraren aikinsu domin sauya su da wasu.

Gwamna Abba ya dakatar da wasu yan jaridu a gidan gwamnati
Gwamnatin Abba Kabir ta kori wasu yan jaridu 14 daga gidan gwamnatin Kano. Hoto: Abba Kabir Yusuf.
Asali: Facebook

Abba ya sallami wasu yan jaridun gidan gwamnati

Kara karanta wannan

Bayan kara kudin fetur, Tinubu ya shirya kakabawa 'yan Najeriya wani sabon haraji

Kakakin Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa shi ya tabbatar da haka a cikin wata sanarwa da Daily Trust ta samu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sai dai Dawakin Tofa bai fayyace dalilin dakatar da yan jaridun ba inda ya umarce su da su bi umarnin da aka ba su.

Dawakin Tofa ya godewa yan jaridun kan irin gudunmawar da suka bayar a cikin shekara daya da watanni da gwamnatin Abba Kabir ta yi.

"Ina amfani da wannan dama wurin yi muku godiya kan gudunmawar da kuka bayar a wannan gwamnati tsawon shekara daya da watanni."
"Abin takaici, lokacin da na ke kasar Serbia wasu abubuwa sun faru da ke buƙatar daukar wasu matakai."
"Wannan ba shi ne karshen mu'amala a tsakaninmu ba, zamu cigaba da tafiya a hukumance ko akasin haka."

Kara karanta wannan

Tsohon gwamna ya bayyana babbar matsalar Najeriya da Tinubu ya fara magancewa

- Cewar sanarwar

Yan jaridun da abin ya shafa a Kano

Daga cikinsu akwai daraktan wayar da kan al'umma, Aliyu Yusuf da jimi'im hulda da jama'a, Sani Suraj Abubakar da Adamu Dabo da ke kai rahoto ga gidan rediyon Pyramid (FRCN).

Sai kuma Naziru Yau daga ARTV da Sadiq Sani AA daga ARTV da Rabiu Sunusi da Umar Sheka daga rediyon Freedom, cewar Premium Times.

Har ila yau, akwai Jabir Dan’abba daga gidan rediyon Nasara sai Labara Sound da Simon daga AIT sai Nasiru Danhaki daga NTA da direbansu, Abdullahi Sule da Murtala Baba Kusa daga gidan rediyon Express da Ibrahim Muazzam daga rediyon Kano.

Abba ya taya Kwankwaso murnar cika shekaru 60

Kun ji cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tura sakon murnar ranar haihuwa ga Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso.

Hakan na zuwa ne duk da yawaitar kiran cewa ya kamata Abba Kabir Yusuf ya bijirewa madugun Kwankwasiyya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.