Yaushe Za a Dawo da Wutar Lantarki a Arewacin Najeriya? TCN Ya yi Bayani

Yaushe Za a Dawo da Wutar Lantarki a Arewacin Najeriya? TCN Ya yi Bayani

  • Kamfanin rarraba wutar lantarki TCN ya yi bayani ga yan kasa kan halin da ake ciki bayan katsewar wutar lantarki a Arewa
  • TCN ya bayyana cewa tun a ranar Lahadi da wuta ta dauke injiniyoyi suke ta kokarin samar da mafita kan lamarin har zuwa yanzu
  • Daukewar lantarkin ta shafi jihohin Arewa maso Gabas da wasu sassa da dama na Arewacin Najeriya tun ranar Litinin da asuba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Arewa - Kamfanin rarraba wutar lantarki na kasa (TCN) ya yi bayani kan halin da ake ciki bayan daukewar wutar lantarki a yankin Arewa.

Tun ranar Litinin da asuba wuta ta katse a yankuna da dama inda al'umma suka koma cikin duhu.

Kara karanta wannan

Bobrisky: Asirin shahararren Ɗan daudu ya tonu yana shirin tserewa a iyakar Najeriya

Lantarki
TCN ya bayyana halin da ake ciki kan katsewar lantarki. Hoto: Kola Sulaimon
Asali: Getty Images

Legit ta tatttaro bayanai da kamfanin TCN ya yi ne a cikin wani sako da ya wallafa a Facebook a safiyar ranar Talata.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Halin da ake ciki bayan dauke lantarki

Kamfanin TCN ya bayyana cewa tun da aka samu katsewar lantarki suka tura injiniyoyi domin shawo kan matsalar.

Sai dai cikin rashin sa'a, tun da suka fara ƙoƙarin shawo kan matsalar ba su gano bakin zaren ba kuma sun cigaba da ƙoƙarin a safiyar ranar Talata.

Kamfanin TCN ya ba yan Najeriya hakuri

Kamfanin TCN ya bayar da hakuri kan katsewar wutar lantarki ga gwamnatin Najeriya da dukkan yan kasa.

TCN ya tabbatar da cewa zai dawo da wutar lantarki a jihohin Arewa da zarar ya gano matsalar da kammala gyara.

Jihohin Arewa da ba su da lantarki

Rahotanni sun nuna cewa katsewar lantarki ta shafi dukkan jihohin Arewa maso Gabashin Najeriya.

Kara karanta wannan

'Ana shan wuya,' Wani babba a APC ya cire kunya ya koka kan mulkin Tinubu

Haka zalika kamfanin TCN ya bayyana cewa lamarin ya shafi yankuna da dama a Arewa maso Yamma.

Abin bai tsaya a nan ba, ya wuce har yankin Arewa ta Tsakiya inda al'umma suka shafe sama da sa'o'i 24 babu lantarki.

TCN na raba wuta ga kasashen Afirka

A wani rahoton, kun ji cewa kamfanin TCN ya bayyana cewa akwai wasu ƙasashen Afirka da yake ba wutar lantarki kuma suna shafe sa'o'i 24 ba tare da katsewa ba.

Lamarin ya jawo ce-ce-ku-ce a tsakanin yan Najeriya inda suke ganin bai kamata a ce wasu ƙasashe na samun wuta sama da yadda suke samu ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng