Ministoci Sun Firgita da Dawowar Tinubu, an Fadi Lokacin da Ake Ganin Zai Kori Wasu

Ministoci Sun Firgita da Dawowar Tinubu, an Fadi Lokacin da Ake Ganin Zai Kori Wasu

  • Rahotanni sun tabbatar da cewa akwai yiwuwar Bola Tinubu ya sallami wasu daga cikin Ministoci a wannan mako
  • Tun bayan dawowarsa a karshen mako, ake hasashen komai zai iya faruwa da wasu Ministoci da masu mukamai
  • Hakan bai rasa nasaba da doguwar ganawa da Tinubu ya yi da hadimarsa a bangaren kula da kokarin masu muƙamai, Hadiza Bala Usman

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Kwanaki kadan da dawowar Bola Tinubu an sake maganar sallamar wasu Ministoci.

Rahotanni sun ce akwai yiwuwar shugaban ya kaddamar da korar Ministocin a wannan mako da muke ciki.

Ana hasashen Tinubu zai yi garambawul a mukaman Ministoci
Bayan doguwar ganawa a jiya Litinin, ana tunanin Bola Tinubu zai kori wasu Ministoci a wannan mako. Hoto: @DOlusegun.
Asali: Facebook

Tinubu ya yi ganawa da Hadiza Bala Usman

Kara karanta wannan

Tsohon gwamna ya bayyana babbar matsalar Najeriya da Tinubu ya fara magancewa

The Guardian ta ce Tinubu ya gana da hadima a bangaren kula da ayyukan Ministocin, Hadiza Bala Usman a jiya Litinin 21 ga watan Oktoban 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hakan bai rasa nasaba da yawan korafi kan mafi yawan Ministoci a wannan gwamnati ta jam'iyyar APC.

Al'umma da dama na nuna damuwa kan rashin katabus na wasu Ministoci ke yi a kasar wanda suka cancanci a sauya su.

Ofishin kula da ayyukan Ministocin da tsare-tsare yana tabbatar da wanda duba zuwa ga kokarin wadanda aka nadan.

Har ila yau, zai kuma ba da bahasi kan Ministan da ya kamata a kora ko kuma a rike a gwamnatin, Vanguard ta ruwaito.

Ana hasashen Bola Tinubu zai kori Ministoci

Bayan dawowar Tinubu a karshen mako, an tabbatar cewa wasu Ministoci sun firgita matuka a jiya Litinin 21 ga watan Oktoban 2024.

Kara karanta wannan

"A rage ciki:" Ministan Tinubu ya ce babu kudi a kasa, ya aikawa magidanta shawara

Majiyoyi daga fadar shugaban kasa sun tabbatar cewa Hadiza Bala Usman ta gabatar da kokarin Ministocin ga Tinubu.

Ministocin sun tsorata ne a jiya Litinin bayan doguwar ganawa da Tinubu ya yi da Hadiza Bala Usman.

Tinubu ya shiga ofis bayan gama hutu

A wani labarin, kun ji cewa Fadar shugaban kasa ta fitar da sanarwa kan halin da ake ciki bayan dawowar shugaba Bola Ahmed Tinubu daga hutu daga ketare .

Hakan na zuwa ne bayan shugaban ƙasar ya iso Najeriya bayan ya shafe mako biyu cikin hutu na musamman Birtaniya da Faransa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.