Ministan Tinubu Ya Fadi Lokacin Kawo Karshen Rikicin Manoma da Makiyaya

Ministan Tinubu Ya Fadi Lokacin Kawo Karshen Rikicin Manoma da Makiyaya

  • Ministan tsaro, Mohammed Badaru Abubakar ya nuna takaicinsa kan rikicin manoma da makiyaya a jihar Plateau
  • Muhammad Badaru ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba gwamnatin tarayya za ta samu ta kawo ƙarshen rikice-rikicen
  • Ministan a buƙaci mutanen yankunan da ke fama da wannan matsala da su haƙura su zauna lafiya da juna a tsakaninsu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Plateau - Ministan tsaro, Mohammed Badaru Abubakar, ya bayyana aniyar gwamnatin tarayya ta kawo ƙarshen rikicin manoma da makiyaya a jihar Plateau

Ministan ya bayyana takaicinsa cewa duk da ƙoƙarin da gwamnati da hukumomin tsaro suke yi na ganin an shawo kan rikicin, wasu ɓata gari na ƙoƙarin haddasa fitina.

Kara karanta wannan

"Ka da ku tsaya baya": Gwamna ya fito ya ba matasan Najeriya muhimmiyar shawara

Badaru ya magantu kan rikicin makiyaya da manoma
Ministan tsaro ya ce gwamnati za ta magance rikicin Fulani da makiyaya a Plateau Hoto: Mohammed Badaru
Asali: Facebook

An yi zama saboda rikicin makiyaya da manoma

Badaru ya bayyana haka ne a ranar Lahadi yayin wani taron sasantawa da masu ruwa da tsaki a birnin Jos na jihar Plateau, cewar rahoton jaridar Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Taron ya kasance tsakanin shugabanni, sarakunan gargajiya da malaman addini daga ƙananan hukumomin Barkin Ladi, Bokkos, Mangu da Riyom na jihar.

Ministan tsaro ya magantu kan rikicin makiyaya

Ministan ya ce gwamnatin tarayya ta damu matuƙa da yadda wasu ke son kawo cikas ga noman da ake yi a halin yanzu, rahoton The Punch ya tabbatar.

Ya kuma bayyana cewa kiran da ake yi na raba al’ummomi bisa ga tsarin ƙabilanci da addini a matsayin abin da zai haifar da tashin hankali nan gaba.

"Gwamnatin tarayya ba za ta yarda da irin wannan buƙatar ba da za ta iya haifar da rarrabuwar kawuna da rashin jituwa a tsakanin ƴan Najeriya. Don haka zama tare ba zaɓi ba ne, wajibi ne."

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu ta yi wa ƴan Najeriya albashir da ASUU ke shirin rufe jami'o'i

"Wannan a bayyane yake kan yadda shugaban ƙasa ya tsaya tsayin daka wajen yaƙi da masu son ɓallewa a kowane ɓangare na ƙasar nan."

- Mohammed Badaru Abubakar

Ministan ya buƙaci mutanen yankunan da su ƙauracewa tashe-tashen hankula, su rungumi zaman lafiya domin tabbatar da ci gaban tattalin arziƙin ƙasar nan.

An farmaki makiyaya a jihar Plateau

A wani labarin kuma, kun ji cewa ƙingiyar makiyaya ta Miyetti Allah ta bayyana yadda wasu miyagun mutane su ka kai wa Fulani makiyaya farmaki a jihar Plateau.

Shugaban ƙungiyar, Babayo Yusuf ne ya tabbatar da hare-haren, ya ce an kashe wasu Fulani a lokacin da su ke kiwo.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng