Kwana Ya Ƙare: Wani Babban Ɗan Sanda Ya Mutu cikin Ofis, An Faɗi Abin da Ya Faru

Kwana Ya Ƙare: Wani Babban Ɗan Sanda Ya Mutu cikin Ofis, An Faɗi Abin da Ya Faru

  • Wani DPO na ƴan sanda a jihar Legas mai kula da caji ofis na Ijanikin, ya riga mu gidan gaskiya ranar Alhamis
  • Rahotanni sun ce CSP Bolaji Olugbenga ya rasu ne bayan ya yanke jiki ya faɗi ba zato ba tsammani a ofishinsa
  • Har yanzu rundunar ƴan sanda ba ta ce uffan ba kan lamarin amma wani ɗan sanda ya fadi abin da ya faru

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Lagos - Shugaban ƴan sandan wanda aka fi sani da DPO na caji ofis ɗin Ijanikin a jihar Legas, CSP Bolaji Olugbenga ya riga mu gidan gaskiya.

Rahotanni sun nuna DPO ya yanke jiki ya faɗi ba zato ba tsammani a ofishinsa kuma rai ya yi halinsa tun kafin a kai ga zuwa asibiti ranar Alhamis.

Kara karanta wannan

"Na cancanta," Sanatan APC ya bayyana shirinsa na neman zama shugaban ƙasa a 2027

Sufetan yan sanda, IGP Kayode.
Wani DPO na ƴan sanda ya kwanta dama a ofis a jihar Legas Hoto: @PoliceNG
Asali: Facebook

Jaridar Daily Trust ta tattaro cewa rasuwar babban ɗan sandan ta jefa jami'an caji ofis din cikin jimami da alhini.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda 'dan sanda ya mutu a ofis

Wani dan sanda da ke aiki a caji ofis ɗin, wanda ya yi magana bisa sharadin a sakaya sunansa, ya ce an kai gawar wannanDPO zuwa dakin ajiyar gawa.

"Kwatsam ya yanke jiki ya faɗi ranar Alhamis kuma mun yi gaggawar kai shi asibiti amma abin takaici rai ya yi halinsa," in ji ɗan sandan.

Har kawo yanzu da muka haɗa wannan rahoton rundunar ƴan sanda reshen jihar ba ta fitar da sanarwa a hukumance kan rasuwar DPO ba.

Karanta wasu labaran ƴan sanda a Najeriya

Kara karanta wannan

"Mu haɗa ƙarfi da ƙarfe," Gwamna ya faɗi hanya 1 da za a yi maganin ƴan bindiga

IGP ya biya diyyar ƴan sandan Kano

A wani labarin kuma IGP Kayode Egbetokun ya ba da diyya ga iyalan ƴan sandan da suka rasu sakamakon hatsarin mota a jihar Kano.

Sufeto Janar na ƴan sandan ya ba da diyyar N10m ga iyalan waɗanda suka rasu tare da N2m ga jami'an da suke jinya a gadon asibiti.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262