"Mu Haɗa Karfi da Karfe," Gwamna Ya Faɗi Hanya 1 da Za a Yi Maganin Ƴan Bindiga

"Mu Haɗa Karfi da Karfe," Gwamna Ya Faɗi Hanya 1 da Za a Yi Maganin Ƴan Bindiga

  • Malam Uba Sani ya ce lokaci ya yi da za a haɗa karfi da ƙarfe domin kawo karshen ƴan bindiga a Arewa maso Yamma
  • Gwamna Uba Sani ya buƙaci a kafa tsarin haɗin guiwa tsakanun jihohin Arewa domin zai taimaka wajen dawo da zaman lafiya
  • Ya kuma yabawa gwamnatin tarayya bisa amincewa da kafa rundunar Operation Fansan Yamma, inda ya ce hakan ya nuna dagaske take

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kaduna - Gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya yi kira da a hada karfi da karfe domin yaki da matsalar rashin tsaro a yankin Arewa maso Yamma.

Gwamna Uba Sani ya nuna cewa lokaci ya yi da za a aje komai a gefe, a haɗa hannu wuri guda wajen yaƙi da ƴan bindiga.

Kara karanta wannan

"Kuna da damar taimakon ƴan Najeriya," Jigon APC ya dura kan Kwankwaso da Atiku

Malam Uba Sani.
Gwamnan Kaduna ya bukaci a hada hannu a yaki da yan bindiga Hoto: Senator Uba Sani
Asali: Facebook

Daily Trust ta tattaro cewa gwamnan ya faɗi haka ne a lokacin da ya karɓi bakuncin ministan tsaro, Mohammed Badaru Abubakar a Kaduna.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Akwai bukatar haɗin guiwa" - Uba Sani

Gwamna Sani ya jaddada bukatar samar da tsarin hadin gwiwa tsakanin jihohin Arewa domin magance matsalar rashin tsaro da ta hana mutane sakat.

Ya yabawa gwamnatin tarayya bisa kafa rundunar hadin gwiwa da Operation Fansan Yamma, inda ya ce hakan ya nuna gwamnati dagaske take.

Uba Sani ya ce wannan ziyara da ya kai ofishin ministan tsaro tana da alaƙa da shirye-shiryen kaddamar da rundunar Operation Fansan Yamma.

Gwamna ya nemi a magance tushen rashin tsaro

Gwamnan ya kuma nanata bukatar magance tushen matsalar tsaro ta hanyar bunƙasa harkokin noma, ilimi, samae da ababen more rayuwa da haɗa kan jama'a.

Kara karanta wannan

Gwamna a Arewa ya juyawa Tinubu baya, ya ce manufofinsa ne suka kawo yunwa

Gwamnan ya roki ministan tsaro da ya duba yiwuwar kawo Operation Safe Haven karkashin runduna ta 1 da ke Kaduna, domin inganta harkar tsaro.

Babaru ya yabawa sojoji a Kaduna

A nasa ɓangaren, ministan tsaro ya tabbatarwa Uba Sani cewa gwamnatin tarayya za ta tallafa masa domin kakkaɓe duk wani nau'in ta'addanci a Kaduna.

Ya kuma yabawa dakarun sojoji bisa namijin ƙoƙarin da suka yi a lokacin da ya kai ziyara runduna ta 1 da sasanin atisayen sojojin sama a Kaduna, Channels tv ta kawo.

Kaduna: Sojoji sun kashe ƴan bindiga

Kuna da labarin dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar hallaka wasu ƴan bindiga mutum biyu har lahira a jihar Kaduna.

Sojojin sun sheƙe ƴan bindigan ne lokacin da suka je ɗaukar kuɗin fansa na wasu mutum huɗu da aka dauke.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262